< Zabura 147 >
1 Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
Chvalte Hospodina, nebo dobré jest zpívati žalmy Bohu našemu, nebo rozkošné jest, a ozdobná jest chvála.
2 Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
Stavitel Jeruzaléma Hospodin, rozptýlený lid Izraelský shromažďuje,
3 Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
Kterýž uzdravuje skroušené srdcem, a uvazuje bolesti jejich,
4 Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
Kterýž sčítá počet hvězd, a každé z nich ze jména povolává.
5 Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
Velikýť jest Pán náš, a nesmírný v síle; rozumnosti jeho není počtu.
6 Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
Pozdvihuje pokorných Hospodin, ale bezbožné snižuje až k zemi.
7 Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
Zpívejte Hospodinu s díkčiněním, zpívejte žalmy Bohu našemu na citaře,
8 Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
Kterýž zastírá nebesa hustými oblaky, nastrojuje zemi déšť, a vyvodí trávu na horách.
9 Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
Kterýž dává hovadům potravu jejich, i mladým krkavcům, kteříž volají k němu.
10 Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
Nemáť v síle koně zalíbení, aniž se kochá v lejtkách muže udatného.
11 Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
Líbost má Hospodin v těch, kteříž se ho bojí, a kteříž doufají v milosrdenství jeho.
12 Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
Chval, Jeruzaléme, Hospodina, chval Boha svého, Sione.
13 Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
Nebo on utvrzuje závory bran tvých, požehnání udílí synům tvým u prostřed tebe.
14 Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
On působí v končinách tvých pokoj, a bělí pšeničnou nasycuje tě.
15 Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
On když vysílá na zemi rozkaz svůj, velmi rychle k vykonání běží slovo jeho.
16 Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
Onť dává sníh jako vlnu, jíním jako popelem posýpá.
17 Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
Hází ledem svým jako skyvami; před zimou jeho kdo ostojí?
18 Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
Vysílaje slovo své, rozpouští je; hned jakž povane větrem svým, anť tekou vody.
19 Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
Zvěstuje slovo své Jákobovi, ustanovení svá a soudy své Izraelovi.
20 Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.
Neučinilť tak žádnému národu, a protož soudů jeho nepoznali. Halelujah.