< Zabura 146 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Luzitisa Yave; Zitisa Yave, a muelꞌama.
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
Ndiela zitisanga Yave mu luzingu luama loso; ndiela yimbidilanga Nzambi ama minzitusu thangu yoso ndizingila.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
Kadi tula diana dieno mu bana ba mintinu, mu batu bobo beti fua, bobo balendi vukisa ko.
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
Pheve awu yawu kuenda buna beti vutuka mu ntoto; zikhanu ziawu zilalikini.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Lusakumunu kuidi mutu wowo widi ti Nzambi yi Yakobi niandi nsadisi andi; wuntulanga diana diandi mu Yave, Nzambi andi,
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
mvangi wu diyilu, ntoto, mbu ayi bibio bidi muna; widi wukuikama mu zithangu zioso.
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
Niandi weti vavila mambu ma bobo beti yamusu, ayi wumvananga bidia kuidi bobo badi nzala; Yave niandi weti totula batu bobo badi mu nloko.
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
Yave weti vana kiezila kuidi phofo, Yave weti vumbula bobo badi bakomvama. Yave weti zola batu basonga.
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
Yave weti sunga nzenza, niandi wunkindisanga muana sana ayi difuola vayi weti kakumukina zinzila zi batu bambimbi.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
Yave wunyalanga mu zithangu zioso. Nzambi aku, a Sioni, mu zitsungi zioso. Luzitisa Yave.