< Zabura 146 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Aleluya. ALABA, oh alma mía, á Jehová.
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
Alabaré á Jehová en mi vida: cantaré salmos á mi Dios mientras viviere.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
No confiéis en los príncipes, ni en hijo de hombre, porque no hay en él salud.
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
Saldrá su espíritu, tornaráse en su tierra: en aquel día perecerán sus pensamientos.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Bienaventurado aquel en cuya ayuda es el Dios de Jacob, cuya esperanza es en Jehová su Dios:
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
El cual hizo los cielos y la tierra, la mar, y todo lo que en ellos hay; que guarda verdad para siempre;
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
Que hace derecho á los agraviados; que da pan á los hambrientos: Jehová suelta á los aprisionados;
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
Jehová abre [los ojos] á los ciegos; Jehová levanta á los caídos; Jehová ama á los justos.
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
Jehová guarda á los extranjeros; al huérfano y á la viuda levanta; y el camino de los impíos trastorna.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
Reinará Jehová para siempre; tu Dios, oh Sión, por generación y generación. Aleluya.

< Zabura 146 >