< Zabura 146 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Alaba, o! alma mía, a Jehová.
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
Alabaré a Jehová en mi vida: diré salmos a mi Dios mientras viviere.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
No confiéis en los príncipes, ni en hijo de hombre; porque no hay en él salud.
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
Saldrá su espíritu, volverse ha el hombre en su tierra: en aquel día perecerán sus pensamientos.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Bienaventurado aquel cuyo ayudador es el Dios de Jacob: cuya esperanza es en Jehová su Dios.
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
El que hizo los cielos y la tierra: la mar, y todo lo que en ello está: el que guarda verdad para siempre:
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
El que hace derecho a los agraviados, el que da pan a los hambrientos: Jehová el que suelta a los aprisionados:
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
Jehová es el que abre los ojos a los ciegos: Jehová el que ama a los justos:
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
Jehová el que guarda a los extranjeros: al huérfano y a la viuda levanta; y el camino de los impíos trastorna.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
Reinará Jehová para siempre: tu Dios, o! Sión, por generación y generación. Alelu- Jah.

< Zabura 146 >