< Zabura 146 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Hvalite Gospoda. Hvali Gospoda, oh moja duša.
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
Medtem ko živim, bom hvalil Gospoda; medtem ko imam kakršen koli obstoj, bom prepeval hvalnice svojemu Bogu.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
Svojega trdnega upanja ne polagaj v prince niti v človeškega sina, v katerem ni pomoči.
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
Njegov dih gre dalje, vrača se k svoji zemlji; na ta isti dan propadejo njegove misli.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Srečen je tisti, ki ima za svojo pomoč Jakobovega Boga, katerega upanje je v Gospodu, njegovemu Bogu,
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
ki je naredil nebo in zemljo, morje in vse, kar je tam notri, ki na veke ohranja resnico,
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
ki izvršuje sodbo za zatiranega, ki daje hrano lačnemu. Gospod osvobaja jetnike,
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
Gospod slepim odpira oči, Gospod dviguje tiste, ki so sklonjeni, Gospod ljubi pravične,
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
Gospod varuje tujce in podpira osirotelega in vdovo, toda pot zlobnih postavlja na glavo.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
Gospod bo kraljeval na veke, celó tvoj Bog, oh Sion, vsem rodovom. Hvalite Gospoda.