< Zabura 146 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Hvali, dušo moja, Gospoda.
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
Hvaliæu Gospoda za života svojega, pjevaæu Bogu svojemu dok me je god.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
Ne uzdajte se u knezove, u sina èovjeèijega, u kojega nema pomoæi.
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
Iziðe iz njega duh, i vrati se u zemlju svoju: taj dan propadnu sve pomisli njegove.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Blago onome, kojemu je pomoænik Bog Jakovljev, kojemu je nadanje u Gospodu, Bogu njegovu,
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
Koji je stvorio nebo i zemlju, more i sve što je u njima; koji drži vjeru uvijek,
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
Èini sud onima, kojima se èini krivo; daje hranu gladnima. Gospod driješi svezane,
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
Gospod otvora oèi slijepcima, podiže oborene, Gospod ljubi pravednike.
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
Gospod èuva došljake, pomaže siroti i udovici; a put bezbožnièki prevraæa.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
Gospod je car dovijeka, Bog tvoj, Sione, od koljena do koljena. Aliluja.