< Zabura 146 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Louvado seja Yah! Louvado seja Yahweh, minha alma.
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
Enquanto eu viver, vou elogiar Iavé. Cantarei louvores ao meu Deus enquanto eu existir.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
Não deposite sua confiança em príncipes, em um filho do homem em quem não há ajuda.
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
Seu espírito parte, e ele retorna à terra. Naquele mesmo dia, seus pensamentos perecem.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Feliz é aquele que tem o Deus de Jacó por sua ajuda, cuja esperança está em Yahweh, seu Deus,
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
que fez o céu e a terra, o mar, e tudo o que há neles; que mantém a verdade para sempre;
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
que executa a justiça para os oprimidos; que dá comida a quem tem fome. Yahweh liberta os prisioneiros.
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
Yahweh abre os olhos dos cegos. Yahweh levanta aqueles que estão curvados. Yahweh ama os justos.
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
Yahweh preserva os estrangeiros. Ele sustenta o órfão de pai e a viúva, mas ele vira o caminho dos malvados de cabeça para baixo.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
Yahweh reinará para sempre; seu Deus, ó Sião, para todas as gerações. Louvado seja Yah!

< Zabura 146 >