< Zabura 146 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Aleluia! Louva ao SENHOR, ó minha alma!
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
Louvarei ao SENHOR durante [toda] a minha vida; cantarei louvores a meu Deus enquanto eu [existir].
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
Não ponhas tua confiança em príncipes; em filhos de homens, em quem não há salvação.
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
O espírito dele [s] sai, e volta para sua terra; naquele mesmo dia seus pensamentos perecem.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Bem-aventurado aquele que [tem] o Deus de Jacó como sua ajuda, cuja esperança está no SENHOR seu Deus;
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
Que fez os céus e a terra, o mar, e tudo o que neles [há]; que guarda a fidelidade para sempre.
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
Que faz juízo aos oprimidos, que dá pão aos famintos; o SENHOR solta aos presos.
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
O SENHOR abre [os olhos] dos cegos; o SENHOR levanta aos abatidos; o SENHOR ama aos justos.
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
O SENHOR guarda os estrangeiros; sustenta o órfão e a viúva; mas põe dificuldades ao caminho dos perversos.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
O SENHOR reinará eternamente. Ó Sião, o teu Deus [reinará] geração após geração. Aleluia!

< Zabura 146 >