< Zabura 146 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Halleluja! Mi sjæl, lova Herren!
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
Eg vil lova Herren so lenge eg liver, syngja lov for min Gud medan eg er til.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
Set ikkje lit til hovdingar, til ein menneskjeson som ikkje kann hjelpa.
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
Fer hans ande ut, so vender han attende til si jord, den dagen er det ute med hans tankar.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Sæl er den som hev Jakobs Gud til hjelp, som vonar på Herren, sin Gud!
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
han som hev skapa himmel og jord, havet og alt som i deim er, han som er trufast til æveleg tid,
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
han som gjev dei nedtyngde rett, han som gjev dei hungrige brød. Herren løyser dei bundne.
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
Herren opnar augo på dei blinde, Herren reiser dei nedbøygde, Herren elskar dei rettferdige,
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
Herren varar dei framande, farlause og enkjor held han uppe, men han villar vegen for dei ugudlege.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
Herren skal vera konge æveleg, din Gud, Sion, frå ætt til ætt. Halleluja!