< Zabura 146 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
alleluia Aggei et Zacchariae
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
lauda anima mea Dominum laudabo Dominum in vita mea psallam Deo meo quamdiu fuero nolite confidere in principibus
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
in filiis hominum quibus non est salus
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
exibit spiritus eius et revertetur in terram suam in illa die peribunt omnes cogitationes eorum
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
beatus cuius Deus Iacob adiutor eius spes eius in Domino Deo ipsius
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
qui fecit caelum et terram mare et omnia quae in eis
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
qui custodit veritatem in saeculum facit iudicium iniuriam patientibus dat escam esurientibus Dominus solvit conpeditos
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
Dominus inluminat caecos Dominus erigit adlisos Dominus diligit iustos
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
Dominus custodit advenas pupillum et viduam suscipiet et viam peccatorum disperdet
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
regnabit Dominus in saecula Deus tuus Sion in generationem et generationem

< Zabura 146 >