< Zabura 146 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Louez l'Éternel! Mon âme, loue l'Éternel!
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
Je louerai l'Éternel tant que je vivrai; je célébrerai mon Dieu tant que j'existerai.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
Ne vous confiez pas dans les grands, ni dans aucun fils d'homme, qui ne saurait délivrer.
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
Son souffle s'en va, il retourne à sa terre, et en ce jour-là ses desseins périssent.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Heureux celui qui a le Dieu de Jacob pour aide, et dont l'attente est en l'Éternel son Dieu,
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
Qui a fait les cieux et la terre, la mer et tout ce qui y est; qui garde la fidélité à toujours;
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
Qui fait droit à ceux qui sont opprimés, qui donne du pain à ceux qui ont faim!
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
L'Éternel délie les captifs; l'Éternel ouvre les yeux des aveugles; l'Éternel redresse ceux qui sont courbés; l'Éternel aime les justes.
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
L'Éternel garde les étrangers; il soutient l'orphelin et la veuve; mais il renverse la voie des méchants.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
L'Éternel régnera éternellement. O Sion, ton Dieu est d'âge en âge! Louez l'Éternel!

< Zabura 146 >