< Zabura 146 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Louez l'Eternel. Mon âme, loue l'Eternel.
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
Je louerai l'Eternel durant ma vie, je psalmodierai à mon Dieu tant que je vivrai.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
Ne vous assurez point sur les principaux [d'entre les peuples, ni] sur [aucun] fils d'homme, à qui [il n'appartient] point de délivrer.
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
Son esprit sort, [et l'homme] retourne en sa terre, [et] en ce jour-là ses desseins périssent.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Ô que bienheureux est celui à qui le [Dieu] Fort de Jacob est en aide, [et] dont l'attente est en l'Eternel son Dieu;
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
Qui a fait les cieux et la terre, la mer, et tout ce qui y est, [et] qui garde la vérité à toujours!
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
Qui fait droit à ceux à qui on fait tort; et qui donne du pain à ceux qui ont faim. L'Eternel délie ceux qui sont liés.
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
L'Eternel ouvre [les yeux] aux aveugles; l'Eternel redresse ceux qui sont courbés; l'Eternel aime les justes.
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
L'Eternel garde les étrangers, il maintient l'orphelin et la veuve, et renverse le train des méchants.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
L'Eternel régnera à toujours. Ô Sion! ton Dieu est d'âge en âge. Louez l'Eternel.

< Zabura 146 >