< Zabura 146 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Louez l’Éternel! Mon âme, loue l’Éternel!
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
Je louerai l’Éternel tant que je vivrai, Je célébrerai mon Dieu tant que j’existerai.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
Ne vous confiez pas aux grands, Aux fils de l’homme, qui ne peuvent sauver.
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
Leur souffle s’en va, ils rentrent dans la terre, Et ce même jour leurs desseins périssent.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Heureux celui qui a pour secours le Dieu de Jacob, Qui met son espoir en l’Éternel, son Dieu!
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
Il a fait les cieux et la terre, La mer et tout ce qui s’y trouve. Il garde la fidélité à toujours.
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
Il fait droit aux opprimés; Il donne du pain aux affamés; L’Éternel délivre les captifs;
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
L’Éternel ouvre les yeux des aveugles; L’Éternel redresse ceux qui sont courbés; L’Éternel aime les justes.
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
L’Éternel protège les étrangers, Il soutient l’orphelin et la veuve, Mais il renverse la voie des méchants.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
L’Éternel règne éternellement; Ton Dieu, ô Sion! Subsiste d’âge en âge! Louez l’Éternel!