< Zabura 146 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Praise Yahweh! With my whole inner being I will praise Yahweh.
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
I will praise Yahweh as long as I am alive; I will sing to praise my God for [the rest of] my life.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
[You people], do not trust in your leaders; do not trust humans because they cannot save/rescue you [from your difficulties/problems].
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
And when they die, their corpses [decay and] become soil again. After they die, they can no longer do the things that they planned to do.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
But those whose helper is the God whom Jacob [worshiped] are happy. The one whom they confidently expect [to help them] is Yahweh, their God.
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
He is the one who created heaven and the earth and the oceans and all [the creatures] that are in them. He always does what he has promised to do.
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
He decides matters fairly for those who are (treated unfairly/oppressed), and he provides food for those who are hungry. He frees those who are in prison.
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
Yahweh enables those who are blind to see again. He lifts up those who have fallen down. He loves righteous [people].
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
Yahweh takes care of those from other countries who live in our land, and he helps widows and orphans. But he gets rid of wicked [people].
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
Yahweh will [continue to] be our king forever; you people of Israel, your God will rule forever! Praise Yahweh!

< Zabura 146 >