< Zabura 146 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Praise ye the LORD! Praise the LORD, O my soul!
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
I will praise the LORD, as long as I live; I will sing praises to my God, while I have my being.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
Put not your trust in princes, In the son of man, in whom is no help!
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
His breath goeth forth; he returneth to the dust; In that very day his plans perish.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Happy is he that hath the God of Jacob for his help; Whose hope is in the LORD, his God;
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
Who made heaven and earth, The sea, and all that is therein; Who keepeth truth for ever;
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
Who executeth judgment for the oppressed; Who giveth food to the hungry. The LORD setteth free the prisoners;
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
The LORD openeth the eyes of the blind; The LORD raiseth up them that are bowed down; The LORD loveth the righteous.
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
The LORD preserveth the strangers; He relieveth the fatherless and the widow; But the way of the wicked he maketh crooked.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
The LORD shall reign for ever; Thy God, O Zion! to all generations! Praise ye the LORD!

< Zabura 146 >