< Zabura 146 >

1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Praise ye the Lord. Praise thou the Lord, O my soule.
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
I will prayse the Lord during my life: as long as I haue any being, I wil sing vnto my God.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
Put not your trust in princes, nor in the sonne of man, for there is none helpe in him.
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
His breath departeth, and he returneth to his earth: then his thoughtes perish.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Blessed is he, that hath the God of Iaakob for his helpe, whose hope is in the Lord his God.
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
Which made heauen and earth, the sea, and all that therein is: which keepeth his fidelitie for euer:
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
Which executeth iustice for the oppressed: which giueth bread to the hungry: the Lord loseth the prisoners.
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
The Lord giueth sight to the blinde: the Lord rayseth vp the crooked: the Lord loueth the righteous.
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
The Lord keepeth the strangers: he relieueth the fatherlesse and widowe: but he ouerthroweth the way of the wicked.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
The Lord shall reigne for euer: O Zion, thy God endureth from generation to generation. Prayse ye the Lord.

< Zabura 146 >