< Zabura 146 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Praise the Lord! With my whole being I praise the Lord!
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
I will praise the Lord while I live; I will sing praises to my God while I have breath.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
Don't put your confidence in human leaders—they cannot save you.
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
Once they breathe no more, they go back to dust. On that very day everything they planned dies with them.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Happy are those who have the God of Jacob to help them—their hope is in the Lord their God—
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
the one who made heaven and earth, and the sea along with everything it contains. He is trustworthy forever.
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
He makes sure the oppressed receive justice. He gives food to the hungry. The Lord sets the prisoners free.
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
The Lord makes the blind see. The Lord lifts up those who are bowed down. The Lord loves those who do what is right.
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
The Lord takes care of strangers among us. He looks after widows and orphans. But he makes life difficult for the wicked.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
The Lord will reign forever. Zion, he will be your God for all generations. Praise the Lord!