< Zabura 146 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Hallelujah! Praise Jehovah, O my soul.
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
As long as I live will I praise Jehovah; I will sing psalms unto my God while I have my being.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
Put not confidence in nobles, in a son of man, in whom there is no salvation.
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
His breath goeth forth, he returneth to his earth; in that very day his purposes perish.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Blessed is he who hath the God of Jacob for his help, whose hope is in Jehovah his God,
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
Who made the heavens and the earth, the sea and all that is therein; who keepeth truth for ever;
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
Who executeth judgment for the oppressed, who giveth bread to the hungry. Jehovah looseth the prisoners;
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
Jehovah openeth [the eyes of] the blind; Jehovah raiseth up them that are bowed down; Jehovah loveth the righteous;
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
Jehovah preserveth the strangers; he lifteth up the fatherless and the widow; but the way of the wicked doth he subvert.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
Jehovah will reign for ever, [even] thy God, O Zion, from generation to generation. Hallelujah!