< Zabura 146 >
1 Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
Praise ye Jehovah. Praise Jehovah, O my soul.
2 Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
While I live I will praise Jehovah. I will sing praises to my God while I have any being.
3 Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
Put not your trust in rulers, nor in the son of man, in whom there is no help.
4 Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
His breath goes forth, he returns to his earth. In that very day his thoughts perish.
5 Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
Happy is he who has the God of Jacob for his help, whose hope is in Jehovah his God,
6 Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
who made heaven and earth, the sea, and all that is in them, who keeps truth forever,
7 Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
who executes justice for the oppressed, who gives food to the hungry. Jehovah releases the prisoners.
8 Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
Jehovah opens the eyes of the blind. Jehovah raises up those who are bowed down. Jehovah loves the righteous.
9 Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
Jehovah preserves the sojourners. He upholds the fatherless and widow. But the way of the wicked he turns upside down.
10 Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.
Jehovah will reign forever, thy God, O Zion, to all generations. Praise ye Jehovah.