< Zabura 145 >
1 Zabura ce ta yabo. Ta Dawuda. Zan ɗaukaka ka, ya Allahna, Sarki; zan yabi sunanka har abada abadin.
Ein Lob Davids. Ich will dich erheben, mein Gott, du König, und deinen Namen loben immer und ewiglich.
2 Kowace rana zan yabe ka in kuma ɗaukaka sunanka har abada abadin.
Ich will dich täglich loben und deinen Namen rühmen immer und ewiglich.
3 Ubangiji da girma yake ya kuma cancanci yabo girmansa ya fi ƙarfin ganewar mutum.
Der HERR ist groß und sehr löblich, und seine Größe ist unausforschlich.
4 Tsara guda za tă yi maganar ayyukanka ga wata tsara; za su yi magana game da manyan ayyukanka.
Kindeskinder werden deine Werke preisen und von deiner Gewalt sagen.
5 Za su yi zancen ɗaukakarka mai daraja, zan kuma yi tunani a kan ayyukanka masu banmamaki.
Ich will reden von deiner herrlichen, schönen Pracht und von deinen Wundern,
6 Za su yi magana game da ikon ayyukanka masu bantsoro, zan kuma yi shelar manyan ayyukanka.
daß man soll sagen von deinen herrlichen Taten und daß man erzähle deine Herrlichkeit;
7 Za su yi bikin yalwar alherinka suka kuma rera adalcinka da farin ciki.
daß man preise deine große Güte und deine Gerechtigkeit rühme.
8 Ubangiji mai alheri da kuma tausayi, mai jinkirin fushi cike kuma da ƙauna.
Gnädig und barmherzig ist der HERR, geduldig und von großer Güte.
9 Ubangiji nagari ne ga duka; yana tausayin dukan abubuwan da ya yi.
Der HERR ist allen gütig und erbarmt sich aller seiner Werke.
10 Dukan abubuwan da ka yi za su yabe ka, ya Ubangiji; tsarkakanka za su ɗaukaka ka.
Es sollen dir danken, HERR, alle deine Werke und deine Heiligen dich loben
11 Za su yi maganar ɗaukakar mulkinka za su kuma yi zancen ikonka,
und die Ehre deines Königreiches rühmen und von deiner Gewalt reden,
12 saboda dukan mutane su san manyan ayyukanka da ɗaukakar darajar mulkinka.
daß den Menschenkindern deine Gewalt kund werde und die herrliche Pracht deines Königreichs.
13 Mulkinka madawwamin mulki ne, sarautarka kuma za tă dawwama cikin dukan zamanai. Ubangiji mai aminci ne ga dukan alkawuransa mai ƙauna kuma ga dukan abubuwan da ya yi.
Dein Reich ist ein ewiges Reich, und deine Herrschaft währet für und für.
14 Ubangiji yana riƙe da dukan waɗanda suka faɗi yana kuma ɗaga dukan waɗanda aka rusunar da su ƙasa.
Der HERR erhält alle, die da fallen, und richtet auf alle, die niedergeschlagen sind.
15 Idanun kowa yana dogara gare ka, kana kuma ba su abincinsu a lokacin da ya dace.
Aller Augen warten auf dich, und du gibst ihnen ihre Speise zu seiner Zeit.
16 Ka buɗe hannunka ka kuma ƙosar da sha’awar kowane abu mai rai.
Du tust deine Hand auf und erfüllst alles, was lebt, mit Wohlgefallen.
17 Ubangiji mai adalci ne cikin dukan hanyoyinsa yana kuma nuna ƙauna ga dukan abubuwan da ya yi.
Der HERR ist gerecht in allen seinen Wegen und heilig in allen seinen Werken.
18 Ubangiji yana kusa da kowa da ya kira gare shi, ga duk wanda ya kira gare shi cikin gaskiya.
Der HERR ist nahe allen, die ihn anrufen, allen, die ihn mit Ernst anrufen.
19 Yakan cika sha’awar waɗanda suke tsoronsa; yakan ji kukansu yă kuma cece su.
Er tut, was die Gottesfürchtigen begehren, und hört ihr Schreien und hilft ihnen.
20 Ubangiji yakan lura da dukan waɗanda suke ƙaunarsa, amma dukan mugaye zai hallaka su.
Der HERR behütet alle, die ihn lieben, und wird vertilgen alle Gottlosen.
21 Bakina zai yi magana cikin yabon Ubangiji. Bari kowace halitta ta yabi sunansa mai tsarki har abada abadin.
Mein Mund soll des HERRN Lob sagen, und alles Fleisch lobe seinen heiligen Namen immer und ewiglich.