< Zabura 145 >

1 Zabura ce ta yabo. Ta Dawuda. Zan ɗaukaka ka, ya Allahna, Sarki; zan yabi sunanka har abada abadin.
Hymne de David. Je veux t’exalter, ô mon Dieu, ô Roi, bénir ton nom jusque dans l’éternité.
2 Kowace rana zan yabe ka in kuma ɗaukaka sunanka har abada abadin.
Chaque jour je te bénirai, je célébrerai ton nom à jamais.
3 Ubangiji da girma yake ya kuma cancanci yabo girmansa ya fi ƙarfin ganewar mutum.
Grand est l’Eternel et justement glorifié, sa grandeur est sans bornes.
4 Tsara guda za tă yi maganar ayyukanka ga wata tsara; za su yi magana game da manyan ayyukanka.
Une génération vante tes œuvres à l’autre, et proclame tes hauts faits.
5 Za su yi zancen ɗaukakarka mai daraja, zan kuma yi tunani a kan ayyukanka masu banmamaki.
La splendeur de ta glorieuse majesté, le détail de tes merveilles, voilà ce que je veux exposer.
6 Za su yi magana game da ikon ayyukanka masu bantsoro, zan kuma yi shelar manyan ayyukanka.
Tous célèbrent la puissance de tes prodiges, et moi aussi je veux annoncer ta grandeur.
7 Za su yi bikin yalwar alherinka suka kuma rera adalcinka da farin ciki.
Ils ne tarissent pas sur la gloire de ta grande bonté, et ils chantent ta justice.
8 Ubangiji mai alheri da kuma tausayi, mai jinkirin fushi cike kuma da ƙauna.
Clément et miséricordieux est l’Eternel, tardif à la colère et abondant en grâce.
9 Ubangiji nagari ne ga duka; yana tausayin dukan abubuwan da ya yi.
L’Eternel est bon pour tous, sa pitié s’étend à toutes ses créatures.
10 Dukan abubuwan da ka yi za su yabe ka, ya Ubangiji; tsarkakanka za su ɗaukaka ka.
Toutes tes œuvres te louent, Seigneur; et tes fidèles adorateurs te bénissent.
11 Za su yi maganar ɗaukakar mulkinka za su kuma yi zancen ikonka,
Ils célèbrent l’honneur de ta royauté, et disent ta puissance,
12 saboda dukan mutane su san manyan ayyukanka da ɗaukakar darajar mulkinka.
pour faire connaître aux fils de l’homme tes hauts faits et l’éclat glorieux de ton règne.
13 Mulkinka madawwamin mulki ne, sarautarka kuma za tă dawwama cikin dukan zamanai. Ubangiji mai aminci ne ga dukan alkawuransa mai ƙauna kuma ga dukan abubuwan da ya yi.
Ta royauté remplit toute l’éternité, et ta domination se prolonge d’âge en âge.
14 Ubangiji yana riƙe da dukan waɗanda suka faɗi yana kuma ɗaga dukan waɗanda aka rusunar da su ƙasa.
L’Eternel soutient tous ceux qui tombent, et redresse ceux qui sont courbés.
15 Idanun kowa yana dogara gare ka, kana kuma ba su abincinsu a lokacin da ya dace.
Tous les yeux se tournent avec espoir vers toi, et, toi, tu leur donnes leur subsistance en temps voulu.
16 Ka buɗe hannunka ka kuma ƙosar da sha’awar kowane abu mai rai.
Tu ouvres la main et rassasies avec bienveillance tout être vivant.
17 Ubangiji mai adalci ne cikin dukan hanyoyinsa yana kuma nuna ƙauna ga dukan abubuwan da ya yi.
L’Eternel est juste en toutes ses voies, et généreux en tous ses actes.
18 Ubangiji yana kusa da kowa da ya kira gare shi, ga duk wanda ya kira gare shi cikin gaskiya.
L’Eternel est proche de tous ceux qui l’invoquent, de tous ceux qui l’appellent avec sincérité.
19 Yakan cika sha’awar waɗanda suke tsoronsa; yakan ji kukansu yă kuma cece su.
Il accomplit les désirs de ses fidèles, entend leurs supplications et leur porte secours.
20 Ubangiji yakan lura da dukan waɗanda suke ƙaunarsa, amma dukan mugaye zai hallaka su.
L’Eternel protège tous ceux qui l’aiment, mais il anéantit tous les impies.
21 Bakina zai yi magana cikin yabon Ubangiji. Bari kowace halitta ta yabi sunansa mai tsarki har abada abadin.
Que ma bouche dise les louanges de l’Eternel, et que toute créature bénisse son saint nom à jamais!

< Zabura 145 >