< Zabura 145 >
1 Zabura ce ta yabo. Ta Dawuda. Zan ɗaukaka ka, ya Allahna, Sarki; zan yabi sunanka har abada abadin.
A song of praise. Of David. I will exalt you, my God, O king: I will praise your name for ever and ever.
2 Kowace rana zan yabe ka in kuma ɗaukaka sunanka har abada abadin.
I will bless you every day: I will praise your name for ever and ever.
3 Ubangiji da girma yake ya kuma cancanci yabo girmansa ya fi ƙarfin ganewar mutum.
Great is the Lord and worthy all praise, his greatness is unsearchable.
4 Tsara guda za tă yi maganar ayyukanka ga wata tsara; za su yi magana game da manyan ayyukanka.
One age to another shall praise your deeds, declaring the mighty things you have done.
5 Za su yi zancen ɗaukakarka mai daraja, zan kuma yi tunani a kan ayyukanka masu banmamaki.
Of your glorious majesty they shall tell, and I will muse of your many wonders.
6 Za su yi magana game da ikon ayyukanka masu bantsoro, zan kuma yi shelar manyan ayyukanka.
Of the might of your terrible acts they shall speak, and the tale of your great deeds I will tell.
7 Za su yi bikin yalwar alherinka suka kuma rera adalcinka da farin ciki.
The fame of your abundant goodness and righteousness they shall pour forth in song.
8 Ubangiji mai alheri da kuma tausayi, mai jinkirin fushi cike kuma da ƙauna.
The Lord is full of grace and pity, patient and rich in loving-kindness.
9 Ubangiji nagari ne ga duka; yana tausayin dukan abubuwan da ya yi.
The Lord is good to all the world, and his pity is over all things that he made.
10 Dukan abubuwan da ka yi za su yabe ka, ya Ubangiji; tsarkakanka za su ɗaukaka ka.
All your works give you thanks, O Lord, and you are blessed of those who love you.
11 Za su yi maganar ɗaukakar mulkinka za su kuma yi zancen ikonka,
They shall speak of your glorious kingdom, and of your might shall they discourse,
12 saboda dukan mutane su san manyan ayyukanka da ɗaukakar darajar mulkinka.
making known to all his mighty acts, and the glorious majesty of his kingdom.
13 Mulkinka madawwamin mulki ne, sarautarka kuma za tă dawwama cikin dukan zamanai. Ubangiji mai aminci ne ga dukan alkawuransa mai ƙauna kuma ga dukan abubuwan da ya yi.
Yours is a kingdom that lives through all ages: through all generations extends your dominion.
14 Ubangiji yana riƙe da dukan waɗanda suka faɗi yana kuma ɗaga dukan waɗanda aka rusunar da su ƙasa.
The Lord upholds all who fall; he lifts up all who are bowed down.
15 Idanun kowa yana dogara gare ka, kana kuma ba su abincinsu a lokacin da ya dace.
The eyes of all look in hope to you, and you give them their food in due season.
16 Ka buɗe hannunka ka kuma ƙosar da sha’awar kowane abu mai rai.
You yourself open your hand, and fill with your favour all things that live.
17 Ubangiji mai adalci ne cikin dukan hanyoyinsa yana kuma nuna ƙauna ga dukan abubuwan da ya yi.
The Lord is righteous in all his ways, gracious is he in all that he does.
18 Ubangiji yana kusa da kowa da ya kira gare shi, ga duk wanda ya kira gare shi cikin gaskiya.
The Lord is near to all who call him, to all who call upon him in truth.
19 Yakan cika sha’awar waɗanda suke tsoronsa; yakan ji kukansu yă kuma cece su.
He will fulfil the desires of those who fear him; he will hear their cry for help and save them.
20 Ubangiji yakan lura da dukan waɗanda suke ƙaunarsa, amma dukan mugaye zai hallaka su.
The Lord is the keeper of all who love him, but all the wicked will he destroy.
21 Bakina zai yi magana cikin yabon Ubangiji. Bari kowace halitta ta yabi sunansa mai tsarki har abada abadin.
My mouth will utter the praise of the Lord, and all life will bless his holy name for ever and ever.