< Zabura 145 >
1 Zabura ce ta yabo. Ta Dawuda. Zan ɗaukaka ka, ya Allahna, Sarki; zan yabi sunanka har abada abadin.
“A hymn of praise by David.” I will extol thee, my God, O king; and I will bless thy name for ever and ever.
2 Kowace rana zan yabe ka in kuma ɗaukaka sunanka har abada abadin.
Every day will I bless thee, and I will praise thy name for ever and ever.
3 Ubangiji da girma yake ya kuma cancanci yabo girmansa ya fi ƙarfin ganewar mutum.
Great is the Lord, and greatly praised, and his greatness is unsearchable.
4 Tsara guda za tă yi maganar ayyukanka ga wata tsara; za su yi magana game da manyan ayyukanka.
One generation shall praise thy works to the other, and thy mighty acts shall they declare.
5 Za su yi zancen ɗaukakarka mai daraja, zan kuma yi tunani a kan ayyukanka masu banmamaki.
On the majestic glory of thy excellence, and on thy wondrous deeds will I meditate.
6 Za su yi magana game da ikon ayyukanka masu bantsoro, zan kuma yi shelar manyan ayyukanka.
And of the might of thy terrible acts shall men converse: and thy greatness will I relate.
7 Za su yi bikin yalwar alherinka suka kuma rera adalcinka da farin ciki.
The memorial of thy abundant goodness shall they loudly proclaim, and they shall sing joyfully of thy righteousness.
8 Ubangiji mai alheri da kuma tausayi, mai jinkirin fushi cike kuma da ƙauna.
Gracious and merciful is the Lord, long-suffering, and great in kindness.
9 Ubangiji nagari ne ga duka; yana tausayin dukan abubuwan da ya yi.
The Lord is good to all, and his mercies are over all his works.
10 Dukan abubuwan da ka yi za su yabe ka, ya Ubangiji; tsarkakanka za su ɗaukaka ka.
All thy works shall thank thee, O Lord; and thy pious servants shall bless thee.
11 Za su yi maganar ɗaukakar mulkinka za su kuma yi zancen ikonka,
Of the glory of thy kingdom shall they converse, and of thy might shall they speak:
12 saboda dukan mutane su san manyan ayyukanka da ɗaukakar darajar mulkinka.
To make known to the sons of men his mighty acts, and the glorious majesty of his kingdom.
13 Mulkinka madawwamin mulki ne, sarautarka kuma za tă dawwama cikin dukan zamanai. Ubangiji mai aminci ne ga dukan alkawuransa mai ƙauna kuma ga dukan abubuwan da ya yi.
Thy kingdom is a kingdom of all eternities, and thy dominion [subsisteth] throughout all generations.
14 Ubangiji yana riƙe da dukan waɗanda suka faɗi yana kuma ɗaga dukan waɗanda aka rusunar da su ƙasa.
The Lord upholdeth all who are falling, and raiseth up all those who are bowed down.
15 Idanun kowa yana dogara gare ka, kana kuma ba su abincinsu a lokacin da ya dace.
The eyes of all wait hopefully upon thee, and thou givest them their food in its due season.
16 Ka buɗe hannunka ka kuma ƙosar da sha’awar kowane abu mai rai.
Thou openest thy hand, and satisfiest the desire of every living thing.
17 Ubangiji mai adalci ne cikin dukan hanyoyinsa yana kuma nuna ƙauna ga dukan abubuwan da ya yi.
Righteous is the Lord in all his ways, and beneficent in all his works.
18 Ubangiji yana kusa da kowa da ya kira gare shi, ga duk wanda ya kira gare shi cikin gaskiya.
The Lord is nigh unto all those who call on him, to all who call on him in truth.
19 Yakan cika sha’awar waɗanda suke tsoronsa; yakan ji kukansu yă kuma cece su.
The desire of those who fear him will he fulfill, and their cry will he hear, and save them.
20 Ubangiji yakan lura da dukan waɗanda suke ƙaunarsa, amma dukan mugaye zai hallaka su.
The Lord preserveth all those who love him; but all the wicked will he destroy.
21 Bakina zai yi magana cikin yabon Ubangiji. Bari kowace halitta ta yabi sunansa mai tsarki har abada abadin.
The praise of the Lord shall my mouth speak: and let all flesh bless his holy name for ever and ever.