< Zabura 145 >

1 Zabura ce ta yabo. Ta Dawuda. Zan ɗaukaka ka, ya Allahna, Sarki; zan yabi sunanka har abada abadin.
The Praise of David himself. I will extol you, O God, my king. And I will bless your name, in this time and forever and ever.
2 Kowace rana zan yabe ka in kuma ɗaukaka sunanka har abada abadin.
Throughout every single day, I will bless you. And I will praise your name, in this time and forever and ever.
3 Ubangiji da girma yake ya kuma cancanci yabo girmansa ya fi ƙarfin ganewar mutum.
The Lord is great and exceedingly praiseworthy. And there is no end to his greatness.
4 Tsara guda za tă yi maganar ayyukanka ga wata tsara; za su yi magana game da manyan ayyukanka.
Generation after generation will praise your works, and they will declare your power.
5 Za su yi zancen ɗaukakarka mai daraja, zan kuma yi tunani a kan ayyukanka masu banmamaki.
They will tell of the magnificent glory of your sanctity. And they will discourse of your wonders.
6 Za su yi magana game da ikon ayyukanka masu bantsoro, zan kuma yi shelar manyan ayyukanka.
And they will talk about the virtue of your terrible acts. And they will describe your greatness.
7 Za su yi bikin yalwar alherinka suka kuma rera adalcinka da farin ciki.
They will shout about the memory of your abundant sweetness. And they will exult in your justice.
8 Ubangiji mai alheri da kuma tausayi, mai jinkirin fushi cike kuma da ƙauna.
The Lord is compassionate and merciful, patient and full of mercy.
9 Ubangiji nagari ne ga duka; yana tausayin dukan abubuwan da ya yi.
The Lord is sweet to all things, and his compassion is upon all his works.
10 Dukan abubuwan da ka yi za su yabe ka, ya Ubangiji; tsarkakanka za su ɗaukaka ka.
O Lord, may all your works confess to you, and let your holy ones bless you.
11 Za su yi maganar ɗaukakar mulkinka za su kuma yi zancen ikonka,
They will speak of the glory of your kingdom, and they will declare your power,
12 saboda dukan mutane su san manyan ayyukanka da ɗaukakar darajar mulkinka.
so as to make known to the sons of men your power and the glory of your magnificent kingdom.
13 Mulkinka madawwamin mulki ne, sarautarka kuma za tă dawwama cikin dukan zamanai. Ubangiji mai aminci ne ga dukan alkawuransa mai ƙauna kuma ga dukan abubuwan da ya yi.
Your kingdom is a kingdom for all ages, and your dominion is with all, from generation to generation. The Lord is faithful in all his words and holy in all his works.
14 Ubangiji yana riƙe da dukan waɗanda suka faɗi yana kuma ɗaga dukan waɗanda aka rusunar da su ƙasa.
The Lord lifts up all who have fallen down, and he sets upright all who have been thrown down.
15 Idanun kowa yana dogara gare ka, kana kuma ba su abincinsu a lokacin da ya dace.
O Lord, all eyes hope in you, and you provide their food in due time.
16 Ka buɗe hannunka ka kuma ƙosar da sha’awar kowane abu mai rai.
You open your hand, and you fill every kind of animal with a blessing.
17 Ubangiji mai adalci ne cikin dukan hanyoyinsa yana kuma nuna ƙauna ga dukan abubuwan da ya yi.
The Lord is just in all his ways and holy in all his works.
18 Ubangiji yana kusa da kowa da ya kira gare shi, ga duk wanda ya kira gare shi cikin gaskiya.
The Lord is near to all who call upon him, to all who call upon him in truth.
19 Yakan cika sha’awar waɗanda suke tsoronsa; yakan ji kukansu yă kuma cece su.
He will do the will of those who fear him, and he will heed their supplication and accomplish their salvation.
20 Ubangiji yakan lura da dukan waɗanda suke ƙaunarsa, amma dukan mugaye zai hallaka su.
The Lord watches over all who love him. And he will destroy all sinners.
21 Bakina zai yi magana cikin yabon Ubangiji. Bari kowace halitta ta yabi sunansa mai tsarki har abada abadin.
My mouth will speak the praise of the Lord, and may all flesh bless his holy name, in this time and forever and ever.

< Zabura 145 >