< Zabura 145 >
1 Zabura ce ta yabo. Ta Dawuda. Zan ɗaukaka ka, ya Allahna, Sarki; zan yabi sunanka har abada abadin.
Jeg vil ophøje dig, min Gud, du som er Kongen! og love dit Navn evindelig og altid.
2 Kowace rana zan yabe ka in kuma ɗaukaka sunanka har abada abadin.
Hver Dag vil jeg love dig og prise dit Navn evindelig og altid.
3 Ubangiji da girma yake ya kuma cancanci yabo girmansa ya fi ƙarfin ganewar mutum.
Herren er stor og saare priselig, og hans Magt er uransagelig.
4 Tsara guda za tă yi maganar ayyukanka ga wata tsara; za su yi magana game da manyan ayyukanka.
En Slægt skal berømme for den anden dine Gerninger, og de skulle forkynde din Vælde.
5 Za su yi zancen ɗaukakarka mai daraja, zan kuma yi tunani a kan ayyukanka masu banmamaki.
Jeg vil betænke din Majestæts herlige Ære og dine underfalde Gerninger.
6 Za su yi magana game da ikon ayyukanka masu bantsoro, zan kuma yi shelar manyan ayyukanka.
Og der skal tales om dine forfærdelige Gerningers Vælde, og jeg vil fortælle om din Magt.
7 Za su yi bikin yalwar alherinka suka kuma rera adalcinka da farin ciki.
De skulle udbrede din store Godheds Ihukommelse og synge med Fryd om din Retfærdighed.
8 Ubangiji mai alheri da kuma tausayi, mai jinkirin fushi cike kuma da ƙauna.
Herren er naadig og barmhjertig, langmodig og af stor Miskundhed.
9 Ubangiji nagari ne ga duka; yana tausayin dukan abubuwan da ya yi.
Herren er god imod alle, og hans Barmhjertighed er over alle hans Gerninger.
10 Dukan abubuwan da ka yi za su yabe ka, ya Ubangiji; tsarkakanka za su ɗaukaka ka.
Dig, Herre! skulle alle dine Gerninger prise og dine hellige love dig.
11 Za su yi maganar ɗaukakar mulkinka za su kuma yi zancen ikonka,
De skulle forkynde dit Riges Ære, tale om din Vælde,
12 saboda dukan mutane su san manyan ayyukanka da ɗaukakar darajar mulkinka.
for at kundgøre for Menneskens Børn hans Vælde og hans Riges herlige Ære.
13 Mulkinka madawwamin mulki ne, sarautarka kuma za tă dawwama cikin dukan zamanai. Ubangiji mai aminci ne ga dukan alkawuransa mai ƙauna kuma ga dukan abubuwan da ya yi.
Dit Rige er et Rige i al Evighed, og dit Herredømme varer fra Slægt til Slægt.
14 Ubangiji yana riƙe da dukan waɗanda suka faɗi yana kuma ɗaga dukan waɗanda aka rusunar da su ƙasa.
Herren opholder alle dem, som falde, og oprejser alle de nedbøjede.
15 Idanun kowa yana dogara gare ka, kana kuma ba su abincinsu a lokacin da ya dace.
Alles Øjne vogte paa dig, og du giver dem deres Spise i sin Tid.
16 Ka buɗe hannunka ka kuma ƙosar da sha’awar kowane abu mai rai.
Du oplader din Haand og mætter alt det, som lever, med Velbehagelighed.
17 Ubangiji mai adalci ne cikin dukan hanyoyinsa yana kuma nuna ƙauna ga dukan abubuwan da ya yi.
Herren er retfærdig i alle sine Veje og miskundelig i alle sine Gerninger.
18 Ubangiji yana kusa da kowa da ya kira gare shi, ga duk wanda ya kira gare shi cikin gaskiya.
Herren er nær hos alle, som kalde paa ham, hos alle, som kalde paa ham i Sandhed.
19 Yakan cika sha’awar waɗanda suke tsoronsa; yakan ji kukansu yă kuma cece su.
Han gør efter deres Velbehagelighed, som ham frygte, og han hører deres Skrig og frelser dem.
20 Ubangiji yakan lura da dukan waɗanda suke ƙaunarsa, amma dukan mugaye zai hallaka su.
Herren bevarer alle dem, som elske ham, men han ødelægger alle de ugudelige.
21 Bakina zai yi magana cikin yabon Ubangiji. Bari kowace halitta ta yabi sunansa mai tsarki har abada abadin.
Min Mund skal udtale Herrens Lov, og alt Kød skal love hans hellige Navn evindelig og altid.