< Zabura 144 >

1 Ta Dawuda. Yabo ya tabbata ga Ubangiji dutsena, wanda ya horar da hannuwana don yaƙi, yatsotsina don faɗa.
Por David. Bendito seja Yahweh, meu rochedo, que treina minhas mãos para a guerra, e meus dedos para lutar...
2 Shi ne Allah mai ƙaunata da kuma kagarata, katangata da mai cetona, garkuwata, wanda nake neman mafaka daga gare shi, wanda ya sa mutane a ƙarƙashina.
minha amorosa gentileza, minha fortaleza, minha torre alta, meu entregador, meu escudo, e aquele em quem me refugio, que submete meu povo sob minhas ordens.
3 Ya Ubangiji, wane ne mutum da ka kula da shi, ɗan mutum da har za ka yi tunaninsa?
Yahweh, o que é o homem, que você se importa com ele? Ou o filho do homem, que você pensa dele?
4 Mutum yana kama da numfashi; kwanakinsa suna wucewa kamar inuwa.
O homem é como um sopro. Seus dias são como uma sombra que passa.
5 Ka tsage sammanka, ya Ubangiji, ka sauko; ka taɓa duwatsu, domin su yi hayaƙi.
Part seus céus, Yahweh, e desça. Toque as montanhas, e eles fumarão.
6 Ka aiko da walƙiya ka watsar da abokan gāba; ka karɓa kibiyoyinka ka sa su gudu.
Jogue fora os relâmpagos e espalhe-os. Envie suas setas, e as roteie.
7 Ka miƙa hannunka daga bisa; ka cece ni ka kuma kuɓutar da ni daga manyan ruwaye, daga hannuwan baƙi
Estenda sua mão de cima, me resgatar, e me tirar de grandes águas, das mãos de estrangeiros,
8 waɗanda bakunansu sun cika da ƙarya, waɗanda hannuwansu na dama masu ruɗu ne.
cujas bocas falam engano, cuja mão direita é uma mão direita de falsidade.
9 Zan rera sabuwar waƙa gare ka, ya Allah; a kan molo mai tsirkiya goma zan yi maka kiɗi,
Vou cantar uma nova canção para você, Deus. Em uma lira de dez cordas, cantarei louvores a você.
10 ga Wannan wanda yake ba wa sarakuna nasara, wanda ya cece bawansa Dawuda. Daga takobin kisa.
Você é aquele que dá a salvação aos reis, que resgata David, seu servo, da espada mortífera.
11 Ka cece ni ka kuma kuɓutar da ni daga hannuwan baƙi waɗanda bakunansu sun cika da ƙarya, waɗanda hannuwansu na dama masu ruɗu ne.
Me resgatar e me livrar das mãos de estrangeiros, cujas bocas falam engano, cuja mão direita é uma mão direita de falsidade.
12 Ta haka’ya’yanmu maza a ƙuruciyarsu za su zama kamar tsire-tsiren da aka kula da su,’ya’yanmu mata kuma za su zama kamar ginshiƙai da sassaƙa don adon fada.
Então nossos filhos serão como plantas bem nutridas, nossas filhas como pilares esculpidos para adornar um palácio.
13 Rumbunanmu za su cika da kowane irin tanadi. Tumakinmu za su ƙaru ninki dubu, ninki dubu goma-goma a filayenmu;
Nossos celeiros estão cheios, cheios de todos os tipos de provisão. Nossas ovelhas produzem milhares e dez mil em nossos campos.
14 shanunmu za su ja kaya masu nauyi. Ba za a sami tashin hankali a katangarmu ba, ba zuwan zaman bauta, ba jin kukan damuwa a titunanmu.
Nossos bois puxarão cargas pesadas. Não há arrombamento e não há como ir embora, e sem alaridos em nossas ruas.
15 Masu albarka ne mutanen da wannan zai zama haka; masu albarka ne mutanen da Allah ne Ubangiji.
Felizes são as pessoas que se encontram em tal situação. Felizes são as pessoas cujo Deus é Yahweh.

< Zabura 144 >