< Zabura 144 >

1 Ta Dawuda. Yabo ya tabbata ga Ubangiji dutsena, wanda ya horar da hannuwana don yaƙi, yatsotsina don faɗa.
De David, à l'occasion de Goliath. Béni soit le Seigneur mon Dieu, qui dresse mes mains à la bataille, et mes doigts à la guerre.
2 Shi ne Allah mai ƙaunata da kuma kagarata, katangata da mai cetona, garkuwata, wanda nake neman mafaka daga gare shi, wanda ya sa mutane a ƙarƙashina.
Ma miséricorde et mon refuge, mon salut, mon défenseur et mon appui, j'ai espéré en Celui qui me soumet mon peuple.
3 Ya Ubangiji, wane ne mutum da ka kula da shi, ɗan mutum da har za ka yi tunaninsa?
Seigneur, qu'est-ce donc que l'homme pour que tu te sois révélé à lui, ou le fils de l'homme pour que tu tienne compte de lui?
4 Mutum yana kama da numfashi; kwanakinsa suna wucewa kamar inuwa.
L'homme est semblable à la vanité même; ses jours passent comme une ombre.
5 Ka tsage sammanka, ya Ubangiji, ka sauko; ka taɓa duwatsu, domin su yi hayaƙi.
Seigneur, incline tes cieux, et descends; touche les montagnes, et elles s'en iront en fumée.
6 Ka aiko da walƙiya ka watsar da abokan gāba; ka karɓa kibiyoyinka ka sa su gudu.
Fais briller des éclairs, et tu les réduiras en poudre; lance tes traits, et tu les troubleras.
7 Ka miƙa hannunka daga bisa; ka cece ni ka kuma kuɓutar da ni daga manyan ruwaye, daga hannuwan baƙi
Envoies d'en haut ta main, délivre-moi, retire-moi des grandes eaux et des mains des fils d'étrangers.
8 waɗanda bakunansu sun cika da ƙarya, waɗanda hannuwansu na dama masu ruɗu ne.
Leur bouche a dit des paroles vaines, et leur droite est une main d'iniquité.
9 Zan rera sabuwar waƙa gare ka, ya Allah; a kan molo mai tsirkiya goma zan yi maka kiɗi,
O Dieu; je te chanterai un cantique nouveau, je chanterai pour toi sur la harpe à dix cordes.
10 ga Wannan wanda yake ba wa sarakuna nasara, wanda ya cece bawansa Dawuda. Daga takobin kisa.
Tu donnes le salut aux rois; tu as sauvé David, ton serviteur, du glaive cruel.
11 Ka cece ni ka kuma kuɓutar da ni daga hannuwan baƙi waɗanda bakunansu sun cika da ƙarya, waɗanda hannuwansu na dama masu ruɗu ne.
Délivre-moi, retire-moi des mains des fils d'étrangers dont la bouche a dit des paroles vaines, et dont la droite est une main d'iniquité.
12 Ta haka’ya’yanmu maza a ƙuruciyarsu za su zama kamar tsire-tsiren da aka kula da su,’ya’yanmu mata kuma za su zama kamar ginshiƙai da sassaƙa don adon fada.
Leurs fils sont comme des rejetons fleurissants en leur jeunesse; leurs filles sont arrangées et parées comme l'idole d'un temple.
13 Rumbunanmu za su cika da kowane irin tanadi. Tumakinmu za su ƙaru ninki dubu, ninki dubu goma-goma a filayenmu;
Leurs celliers sont massifs, regorgeant de telle chose et de telle autre; leurs brebis sont fécondes, et se multiplient dans leurs pacages.
14 shanunmu za su ja kaya masu nauyi. Ba za a sami tashin hankali a katangarmu ba, ba zuwan zaman bauta, ba jin kukan damuwa a titunanmu.
Leurs bœufs sont gras; leurs murs n'ont ni éboulements ni brèches; on n'entend pas de cris dans leurs demeures.
15 Masu albarka ne mutanen da wannan zai zama haka; masu albarka ne mutanen da Allah ne Ubangiji.
Heureux, disent-ils, le peuple qui a de tels biens: mais plus heureux le peuple dont le Seigneur est le Dieu!

< Zabura 144 >