< Zabura 144 >

1 Ta Dawuda. Yabo ya tabbata ga Ubangiji dutsena, wanda ya horar da hannuwana don yaƙi, yatsotsina don faɗa.
I praise Yahweh, who is [like an overhanging] rock [under which I] ([get refuge/am protected])! He trains my hands so that I can use them to fight battles; he trains my fingers so that I can [shoot arrows in a war].
2 Shi ne Allah mai ƙaunata da kuma kagarata, katangata da mai cetona, garkuwata, wanda nake neman mafaka daga gare shi, wanda ya sa mutane a ƙarƙashina.
He is the one who protects me; he is [like] a fortress [DOU] in which I am safe, he protects me [like] [protect soldiers] [MET], and he gives me refuge. He defeats [other] nations and [then] puts them under my power.
3 Ya Ubangiji, wane ne mutum da ka kula da shi, ɗan mutum da har za ka yi tunaninsa?
Yahweh, [we] people are [very insignificant/unimportant], so why (are you concerned/do you care about us) [RHQ]? [It is amazing to me that] you pay attention to humans.
4 Mutum yana kama da numfashi; kwanakinsa suna wucewa kamar inuwa.
[The time that we live is as short] as [SIM] a puff of wind; our time to live disappears like a shadow does.
5 Ka tsage sammanka, ya Ubangiji, ka sauko; ka taɓa duwatsu, domin su yi hayaƙi.
Yahweh, (tear open/open up) the sky and come down! Touch the mountains in order that smoke will pour out from them!
6 Ka aiko da walƙiya ka watsar da abokan gāba; ka karɓa kibiyoyinka ka sa su gudu.
Cause lightning to flash with the result that [your enemies] will run away! Shoot your arrows [at them] and cause them to (run away/scatter).
7 Ka miƙa hannunka daga bisa; ka cece ni ka kuma kuɓutar da ni daga manyan ruwaye, daga hannuwan baƙi
[It is as though my enemies surround me like] a flood; reach your hand down from heaven and rescue me from them [SYN]. They are men from other countries
8 waɗanda bakunansu sun cika da ƙarya, waɗanda hannuwansu na dama masu ruɗu ne.
who [SYN] [always] tell lies. [Even in a courtroom where they swear to tell the truth] they tell lies.
9 Zan rera sabuwar waƙa gare ka, ya Allah; a kan molo mai tsirkiya goma zan yi maka kiɗi,
God, I will sing a new song to you, and I will play my ten-stringed harp [while I sing] to you.
10 ga Wannan wanda yake ba wa sarakuna nasara, wanda ya cece bawansa Dawuda. Daga takobin kisa.
You enable kings to defeat [their enemies]; and you rescued me, your servant David, from [being killed by] my enemies’ swords.
11 Ka cece ni ka kuma kuɓutar da ni daga hannuwan baƙi waɗanda bakunansu sun cika da ƙarya, waɗanda hannuwansu na dama masu ruɗu ne.
[So I ask you to] save me from [being killed by] the swords [that those] evil [people carry]. Rescue me from the power [MTY] of those foreigners who [SYN] [always] tell lies, and [who raise] their right hands [in courtrooms when they solemnly declare that they will tell the truth].
12 Ta haka’ya’yanmu maza a ƙuruciyarsu za su zama kamar tsire-tsiren da aka kula da su,’ya’yanmu mata kuma za su zama kamar ginshiƙai da sassaƙa don adon fada.
I wish/hope that our young sons will grow up to be like strong plants [SIM], and I wish/hope that our daughters will [grow up to] be [straight and tall] like the pillars [SIM] that stand in the corners of palaces.
13 Rumbunanmu za su cika da kowane irin tanadi. Tumakinmu za su ƙaru ninki dubu, ninki dubu goma-goma a filayenmu;
I wish/hope that our barns will be full of many different crops. I wish/hope that the sheep in our fields will give birth to tens of thousands of baby lambs.
14 shanunmu za su ja kaya masu nauyi. Ba za a sami tashin hankali a katangarmu ba, ba zuwan zaman bauta, ba jin kukan damuwa a titunanmu.
I wish/hope that our cows will give birth to many calves without having any miscarriages or deaths when they are born (OR, that no enemies will break through our city walls and take us (into exile/to their own countries)). I wish/hope that [there will not be a time when the people in] our streets cry out in distress [because foreign armies are invading].
15 Masu albarka ne mutanen da wannan zai zama haka; masu albarka ne mutanen da Allah ne Ubangiji.
If good things like that happen to a nation, the people will be very happy. The people whose God is Yahweh are the ones who will be happy!

< Zabura 144 >