< Zabura 144 >

1 Ta Dawuda. Yabo ya tabbata ga Ubangiji dutsena, wanda ya horar da hannuwana don yaƙi, yatsotsina don faɗa.
Blessed be the LORD, my rock, Who teacheth my hands to war, And my fingers to fight!
2 Shi ne Allah mai ƙaunata da kuma kagarata, katangata da mai cetona, garkuwata, wanda nake neman mafaka daga gare shi, wanda ya sa mutane a ƙarƙashina.
He who is my loving-kindness and my fortress; My high tower and my deliverer, My shield, and he in whom I trust; Who subdueth peoples under me.
3 Ya Ubangiji, wane ne mutum da ka kula da shi, ɗan mutum da har za ka yi tunaninsa?
LORD, what is man, that thou art mindful of him, Or the son of man, that thou makest account of him?
4 Mutum yana kama da numfashi; kwanakinsa suna wucewa kamar inuwa.
Man is like a vapor; His day is like a shadow that passeth away.
5 Ka tsage sammanka, ya Ubangiji, ka sauko; ka taɓa duwatsu, domin su yi hayaƙi.
Bow thy heavens, O LORD! and come down; Touch the mountains, so that they shall smoke!
6 Ka aiko da walƙiya ka watsar da abokan gāba; ka karɓa kibiyoyinka ka sa su gudu.
Cast forth lightnings, and scatter them; Shoot forth thine arrows, and destroy them!
7 Ka miƙa hannunka daga bisa; ka cece ni ka kuma kuɓutar da ni daga manyan ruwaye, daga hannuwan baƙi
Send forth thine hand from above; Rescue and save me from deep waters; From the hands of aliens,
8 waɗanda bakunansu sun cika da ƙarya, waɗanda hannuwansu na dama masu ruɗu ne.
Whose mouth uttereth deceit, And whose right hand is a right hand of falsehood!
9 Zan rera sabuwar waƙa gare ka, ya Allah; a kan molo mai tsirkiya goma zan yi maka kiɗi,
I will sing to thee a new song, O God! Upon a ten-stringed psaltery will I sing praise to thee;
10 ga Wannan wanda yake ba wa sarakuna nasara, wanda ya cece bawansa Dawuda. Daga takobin kisa.
To thee, who givest salvation to kings, Who deliverest David, thy servant, from the destructive sword!
11 Ka cece ni ka kuma kuɓutar da ni daga hannuwan baƙi waɗanda bakunansu sun cika da ƙarya, waɗanda hannuwansu na dama masu ruɗu ne.
Rescue and deliver me from the hands of aliens, Whose mouth uttereth deceit, And whose right hand is a right hand of falsehood!
12 Ta haka’ya’yanmu maza a ƙuruciyarsu za su zama kamar tsire-tsiren da aka kula da su,’ya’yanmu mata kuma za su zama kamar ginshiƙai da sassaƙa don adon fada.
That our sons may be as plants, Grown up in their youth; Our daughters as corner-pillars, Hewn like those of a palace!
13 Rumbunanmu za su cika da kowane irin tanadi. Tumakinmu za su ƙaru ninki dubu, ninki dubu goma-goma a filayenmu;
That our garners may be full, Affording all kinds of store; That our sheep may bring forth thousands And ten thousands in our streets.
14 shanunmu za su ja kaya masu nauyi. Ba za a sami tashin hankali a katangarmu ba, ba zuwan zaman bauta, ba jin kukan damuwa a titunanmu.
That our cattle may be fruitful; That there be no breaking in, or going out; And no outcry in our streets.
15 Masu albarka ne mutanen da wannan zai zama haka; masu albarka ne mutanen da Allah ne Ubangiji.
Happy the people that is in such a state! Yea, happy the people whose God is Jehovah!

< Zabura 144 >