< Zabura 144 >

1 Ta Dawuda. Yabo ya tabbata ga Ubangiji dutsena, wanda ya horar da hannuwana don yaƙi, yatsotsina don faɗa.
Hina Gode da na Gaga: sudafa! Ema nodoma! E da na gegema: ne adoba: sa. Amola na gegema: ne momagesa.
2 Shi ne Allah mai ƙaunata da kuma kagarata, katangata da mai cetona, garkuwata, wanda nake neman mafaka daga gare shi, wanda ya sa mutane a ƙarƙashina.
E da na gagulasa amola na gaga: sa. E da na ougiha aligisu dunu esala, amola na gaga: su dunu esala. Na da se mae nabawane hahawane masa: ne, Ea hou dafawaneyale dawa: sa. E da niha fifi asi gala banenesisa
3 Ya Ubangiji, wane ne mutum da ka kula da shi, ɗan mutum da har za ka yi tunaninsa?
Hina Gode! Osobo bagade dunu ilia da hamedei agoai galebe. Dia abuliba: le ilima asigibala: ?
4 Mutum yana kama da numfashi; kwanakinsa suna wucewa kamar inuwa.
Ninia da fo fonomene agoai ba: sa. Ninia esalebe eso da baba bobaligilalebe agoai ba: sa.
5 Ka tsage sammanka, ya Ubangiji, ka sauko; ka taɓa duwatsu, domin su yi hayaƙi.
Hina Gode! Mu gadelale fasili, gudu sa: ima! Goumi digili ba: ma! Amasea, goumi da mobi bubugilalebe ba: mu.
6 Ka aiko da walƙiya ka watsar da abokan gāba; ka karɓa kibiyoyinka ka sa su gudu.
Dia ha lai afagogoma: ne, ha: ha: na gala: su iasima. Dia ha lai dunu hobeama: ne, dadia gala: le se bobogema.
7 Ka miƙa hannunka daga bisa; ka cece ni ka kuma kuɓutar da ni daga manyan ruwaye, daga hannuwan baƙi
Na da hano lugudua mogo sososa. Dia gadodili, lobo ligia guduli, na hiougia gadoma. Ga fi dunu ilia gasaga na hasalasa: besa: le, Dia gaga: ma.
8 waɗanda bakunansu sun cika da ƙarya, waɗanda hannuwansu na dama masu ruɗu ne.
Ilia da dafawane sia: hamedafa sia: sa. Amola ilia hamomusa: ilegele sia: sea, ogogosa.
9 Zan rera sabuwar waƙa gare ka, ya Allah; a kan molo mai tsirkiya goma zan yi maka kiɗi,
Gode! Na da Dima gesami gaheabolo hea: mu. Na da sani baidama dusa, Dima gesami hea: mu.
10 ga Wannan wanda yake ba wa sarakuna nasara, wanda ya cece bawansa Dawuda. Daga takobin kisa.
Di da hina bagade ilia ha lai hasalasima: ne hamosa. Amola Dia hawa: hamosu dunu Da: ibidi gaga: sa.
11 Ka cece ni ka kuma kuɓutar da ni daga hannuwan baƙi waɗanda bakunansu sun cika da ƙarya, waɗanda hannuwansu na dama masu ruɗu ne.
Na dodona: gi ha lai dunu da na osa: la heda: sa: besa: le, Dia na gaga: ma. Ga fi dunu ilia gasaga na hasalasa: besa: le, Dia gaga: ma. Ilia da dafawane sia: hamedafa sia: sa. Amola ilia hamomusa: ilegele sia: sea, ogogosa.
12 Ta haka’ya’yanmu maza a ƙuruciyarsu za su zama kamar tsire-tsiren da aka kula da su,’ya’yanmu mata kuma za su zama kamar ginshiƙai da sassaƙa don adon fada.
Ninia dunu mano ayeligi amolali, da ha: i manu bugi nasegagini heda: be agoai ganumu da defea. Amola ninia idiwilali, ilia da noga: le lelu duni bugi amo da hina bagade ea diasu hegomaia nina: hamonanebe, amo agoai ba: mu da defea.
13 Rumbunanmu za su cika da kowane irin tanadi. Tumakinmu za su ƙaru ninki dubu, ninki dubu goma-goma a filayenmu;
Ninia liligi legesu diasu ilia ha: i manu amoga nabai ba: mu da defea. Ninia sibi amo da nasegagi sogega esalebe, ilia mano osea: idafa lalelegemu da defea.
14 shanunmu za su ja kaya masu nauyi. Ba za a sami tashin hankali a katangarmu ba, ba zuwan zaman bauta, ba jin kukan damuwa a titunanmu.
Ninia bulamagau da mae daba: me asili, mano osea: idafa lalelegemu da defea. Ninia moilai logo ganodini, se nabasu wele sia: su hame nabimu da defea.
15 Masu albarka ne mutanen da wannan zai zama haka; masu albarka ne mutanen da Allah ne Ubangiji.
Fifi asi afae da amo hou ba: sea, hahawane bagade ganumu. Amola ilia da Hina Gode amo ilia Godedafa ilegesea, ilia da hahawane bagade ganumu.

< Zabura 144 >