< Zabura 143 >

1 Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, ka ji addu’ata, ka saurari kukata don neman jinƙai; cikin amincinka da adalcinka ka amsa mini.
Псалом Давидів.
2 Kada ka gabatar da bawanka a gaban shari’a, gama babu wani mai rai da yake adali a gabanka.
І на суд не вступай із рабом Своїм, — бо жоден живий перед обличчям Твоїм справедли́вим не буде!
3 Abokin gāba yana fafarata, ya murƙushe ni har ƙasa; ya sa ina zama a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu tun tuni.
Бо неприятель переслідує душу мою, то́пче живую мою до землі. Посадив мене в те́мряву, як мерці́в цього світу!
4 Ta haka ƙarfina ya ƙare a cikina zuciyata ta damu ƙwarai.
Омліває мій дух у мені, кам'яні́є в нутрі́ моїм серце моє.
5 Na tuna da kwanakin baya na yi tunani a kan dukan ayyukanka na kuma lura da abin da hannuwanka suka yi.
Я згадую дні старода́вні, над усі́ми Твоїми чинами розду́мую, говорю́ про діла́ Твоїх рук.
6 Na buɗe hannuwana gare ka; raina yana jin ƙishinka kamar busasshiyar ƙasa. (Sela)
Я ру́ки свої простягаю до Тебе, душа моя пра́гне Тебе, як ́ пересо́хла земля! (Се́ла)
7 Ka amsa mini da sauri, ya Ubangiji; ƙarfina ya ƙare. Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni in ba haka ba zan zama kamar waɗanda suka gangara zuwa rami.
Поспіши́ мене ви́слухати, Господи, — дух мій кінча́ється! Не ховай Ти від мене обличчя Свого́, і нехай я не бу́ду подібний до тих, хто схо́дить до гро́бу!
8 Bari safiya ta kawo mini maganar ƙaunarka marar ƙarewa, gama na sa zuciyata a gare ka. Ka nuna mini hanyar da zan bi, gama a gare ka na miƙa raina.
Об'яви́ мені вранці Своє милосердя, бо на Тебе наді́юсь, повідо́м Ти мене про дорогу, якою я маю ходи́ти, бо до Тебе підно́шу я душу свою́!
9 Ka cece ni daga abokan gābana, ya Ubangiji, gama na ɓoye kaina a gare ka.
Урятуй мене, Господи, від моїх ворогів, бо до Тебе вдаю́ся!
10 Ka koya mini in yi nufinka, gama kai ne Allahna; bari nagarin Ruhunka yă bi da ni a ƙasar da ba gargaɗa.
Навчи мене волю чинити Твою́, бо Ти Бог мій, — добрий Дух Твій нехай попрова́дить мене по рі́вній землі!
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka kiyaye raina; a cikin adalcinka, ka fid da ni daga wahala.
Ради Ймення Свого, о Господи, оживи мене, Своєю правдою ви́веди душу мою від недолі!
12 A cikin ƙaunarka marar ƙarewa, ka rufe bakunan abokan gābana; ka hallaka dukan maƙiyana, gama ni bawanka ne.
А в Своїм милосерді понищ моїх ворогів, і ви́губи всіх, хто нена́видить душу мою, бо я — раб Твій!

< Zabura 143 >