< Zabura 143 >

1 Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, ka ji addu’ata, ka saurari kukata don neman jinƙai; cikin amincinka da adalcinka ka amsa mini.
A Psalm of David. Hear my prayer, O LORD; give ear to my supplications: in thy faithfulness answer me, [and] in thy righteousness.
2 Kada ka gabatar da bawanka a gaban shari’a, gama babu wani mai rai da yake adali a gabanka.
And enter not into judgment with thy servant; for in thy sight shall no man living be justified.
3 Abokin gāba yana fafarata, ya murƙushe ni har ƙasa; ya sa ina zama a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu tun tuni.
For the enemy hath persecuted my soul; he hath smitten my life down to the ground: he hath made me to dwell in dark places, as those that have been long dead.
4 Ta haka ƙarfina ya ƙare a cikina zuciyata ta damu ƙwarai.
Therefore is my spirit overwhelmed within me; my heart within me is desolate.
5 Na tuna da kwanakin baya na yi tunani a kan dukan ayyukanka na kuma lura da abin da hannuwanka suka yi.
I remember the days of old; I meditate on all thy doings: I muse on the work of thy hands.
6 Na buɗe hannuwana gare ka; raina yana jin ƙishinka kamar busasshiyar ƙasa. (Sela)
I spread forth my hands unto thee: my soul [thirsteth] after thee, as a weary land. (Selah)
7 Ka amsa mini da sauri, ya Ubangiji; ƙarfina ya ƙare. Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni in ba haka ba zan zama kamar waɗanda suka gangara zuwa rami.
Make haste to answer me, O LORD; my spirit faileth: hide not thy face from me; lest I become like them that go down into the pit.
8 Bari safiya ta kawo mini maganar ƙaunarka marar ƙarewa, gama na sa zuciyata a gare ka. Ka nuna mini hanyar da zan bi, gama a gare ka na miƙa raina.
Cause me to hear thy lovingkindness in the morning; for in thee do I trust: cause me to know the way wherein I should walk; for I lift up my soul unto thee.
9 Ka cece ni daga abokan gābana, ya Ubangiji, gama na ɓoye kaina a gare ka.
Deliver me, O LORD, from mine enemies: I flee unto thee to hide me.
10 Ka koya mini in yi nufinka, gama kai ne Allahna; bari nagarin Ruhunka yă bi da ni a ƙasar da ba gargaɗa.
Teach me to do thy will; for thou art my God: thy spirit is good; lead me in the land of uprightness.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka kiyaye raina; a cikin adalcinka, ka fid da ni daga wahala.
Quicken me, O LORD, for thy name’s sake: in thy righteousness bring my soul out of trouble.
12 A cikin ƙaunarka marar ƙarewa, ka rufe bakunan abokan gābana; ka hallaka dukan maƙiyana, gama ni bawanka ne.
And in thy lovingkindness cut off mine enemies, and destroy all them that afflict my soul; for I am thy servant.

< Zabura 143 >