< Zabura 143 >

1 Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, ka ji addu’ata, ka saurari kukata don neman jinƙai; cikin amincinka da adalcinka ka amsa mini.
Hear my prayer, O LORD, give ear to my supplications: in your faithfulness answer me, and in your righteousness.
2 Kada ka gabatar da bawanka a gaban shari’a, gama babu wani mai rai da yake adali a gabanka.
And enter not into judgment with your servant: for in your sight shall no man living be justified.
3 Abokin gāba yana fafarata, ya murƙushe ni har ƙasa; ya sa ina zama a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu tun tuni.
For the enemy has persecuted my soul; he has smitten my life down to the ground; he has made me to dwell in darkness, as those that have been long dead.
4 Ta haka ƙarfina ya ƙare a cikina zuciyata ta damu ƙwarai.
Therefore is my spirit overwhelmed within me; my heart within me is desolate.
5 Na tuna da kwanakin baya na yi tunani a kan dukan ayyukanka na kuma lura da abin da hannuwanka suka yi.
I remember the days of old; I meditate on all your works; I meditate on the work of your hands.
6 Na buɗe hannuwana gare ka; raina yana jin ƙishinka kamar busasshiyar ƙasa. (Sela)
I stretch forth my hands unto you: my soul thirsts after you, as a thirsty land. (Selah)
7 Ka amsa mini da sauri, ya Ubangiji; ƙarfina ya ƙare. Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni in ba haka ba zan zama kamar waɗanda suka gangara zuwa rami.
Hear me speedily, O LORD: my spirit fails: hide not your face from me, lest I be like unto them that go down into the pit.
8 Bari safiya ta kawo mini maganar ƙaunarka marar ƙarewa, gama na sa zuciyata a gare ka. Ka nuna mini hanyar da zan bi, gama a gare ka na miƙa raina.
Cause me to hear your loving kindness in the morning; for in you do I trust: cause me to know the way wherein I should walk; for I lift up my soul unto you.
9 Ka cece ni daga abokan gābana, ya Ubangiji, gama na ɓoye kaina a gare ka.
Deliver me, O LORD, from mine enemies: I flee unto you to hide me.
10 Ka koya mini in yi nufinka, gama kai ne Allahna; bari nagarin Ruhunka yă bi da ni a ƙasar da ba gargaɗa.
Teach me to do your will; for you are my God: your spirit is good; lead me into the land of uprightness.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka kiyaye raina; a cikin adalcinka, ka fid da ni daga wahala.
Restore life in me, O LORD, for your name's sake: for your righteousness' sake bring my soul out of trouble.
12 A cikin ƙaunarka marar ƙarewa, ka rufe bakunan abokan gābana; ka hallaka dukan maƙiyana, gama ni bawanka ne.
And of your mercy cut off mine enemies, and destroy all them that afflict my soul: for I am your servant.

< Zabura 143 >