< Zabura 142 >

1 Maskil ne ta Dawuda. Sa’ad da yake cikin kogo. Addu’a ce. Na yi kuka mai ƙarfi ga Ubangiji; na tā da muryata ga Ubangiji neman jinƙai.
Intelligence de David, lorsqu’il était dans la caverne, prière. De ma voix vers le Seigneur j’ai crié: de ma voix au Seigneur j’ai adressé ma supplication;
2 Na kawo gunagunina a gabansa; a gabansa na faɗa wahalata.
Je répands, en sa présence, ma prière; et ma tribulation, c’est devant lui-même que je l’expose.
3 Sa’ad da ƙarfina ya kāre a cikina, kai ne wanda ya san hanyata. A hanyar da nake tafiya mutane sun kafa mini tarko.
Pendant que mon esprit se retire de moi, et c’est vous qui avez connu mes sentiers.
4 Duba ta damata ka gani; babu wanda ya kula da ni. Ba ni da mafaka; babu wanda ya kula da raina.
Je considérais à ma droite, et je regardais; et il n’y avait personne qui me connût.
5 Na yi kuka gare ka, ya Ubangiji; Na ce, “Kai ne mafakata, rabona a ƙasar masu rai.”
J’ai crié vers vous, Seigneur, j’ai dit: C’est vous qui êtes mon espérance, ma part dans la terre des vivants.
6 Ka saurari kukata, gama ina cikin matsananciyar bukata; ka cece ni daga waɗanda suke fafarata, gama sun fi ni ƙarfi sosai.
Soyez attentif à ma supplication, parce que j’ai, été humilié à l’excès.
7 Ka’yantar da ni daga kurkuku, don in yabi sunanka. Ta haka masu adalci za su taru kewaye da ni saboda alherinka gare ni.
Retirez de la prison mon âme, pour qu’elle glorifie votre nom: des justes m’attendent, jusqu’à ce que vous me rendiez justice.

< Zabura 142 >