< Zabura 142 >
1 Maskil ne ta Dawuda. Sa’ad da yake cikin kogo. Addu’a ce. Na yi kuka mai ƙarfi ga Ubangiji; na tā da muryata ga Ubangiji neman jinƙai.
AN INSTRUCTION OF DAVID. A PRAYER WHEN HE IS IN THE CAVE. My voice [is] to YHWH, I cry, My voice [is] to YHWH, I beg [for] grace.
2 Na kawo gunagunina a gabansa; a gabansa na faɗa wahalata.
I pour forth my meditation before Him, I declare my distress before Him.
3 Sa’ad da ƙarfina ya kāre a cikina, kai ne wanda ya san hanyata. A hanyar da nake tafiya mutane sun kafa mini tarko.
When my spirit has been feeble in me, Then You have known my path; In the way [in] which I walk, They have hid a snare for me.
4 Duba ta damata ka gani; babu wanda ya kula da ni. Ba ni da mafaka; babu wanda ya kula da raina.
Looking on the right hand—and seeing, And I have none recognizing; Refuge has perished from me, There is none inquiring for my soul.
5 Na yi kuka gare ka, ya Ubangiji; Na ce, “Kai ne mafakata, rabona a ƙasar masu rai.”
I have cried to you, O YHWH, I have said, “You [are] my refuge, My portion in the land of the living.”
6 Ka saurari kukata, gama ina cikin matsananciyar bukata; ka cece ni daga waɗanda suke fafarata, gama sun fi ni ƙarfi sosai.
Attend to my loud cry, For I have become very low, Deliver me from my pursuers, For they have been stronger than I.
7 Ka’yantar da ni daga kurkuku, don in yabi sunanka. Ta haka masu adalci za su taru kewaye da ni saboda alherinka gare ni.
Bring forth my soul from prison to confess Your Name, The righteous surround me about, When You confer benefits on me!