< Zabura 142 >

1 Maskil ne ta Dawuda. Sa’ad da yake cikin kogo. Addu’a ce. Na yi kuka mai ƙarfi ga Ubangiji; na tā da muryata ga Ubangiji neman jinƙai.
[A Psalm] of instruction for David, when he was in the cave, —a Prayer. I cried to the Lord with my voice; with my voice I made supplication to the Lord.
2 Na kawo gunagunina a gabansa; a gabansa na faɗa wahalata.
I will pour out before him my supplication: I will declare before him mine affliction.
3 Sa’ad da ƙarfina ya kāre a cikina, kai ne wanda ya san hanyata. A hanyar da nake tafiya mutane sun kafa mini tarko.
When my spirit was fainting within me, then you knew my paths; in the very way wherein I was walking, they hid a snare for me.
4 Duba ta damata ka gani; babu wanda ya kula da ni. Ba ni da mafaka; babu wanda ya kula da raina.
I looked on [my] right hand, and behold, for there was none that noticed me; refuge failed me; and there was none that cared for my soul.
5 Na yi kuka gare ka, ya Ubangiji; Na ce, “Kai ne mafakata, rabona a ƙasar masu rai.”
I cried to you, O Lord, and said, You are my hope, my portion in the land of the living.
6 Ka saurari kukata, gama ina cikin matsananciyar bukata; ka cece ni daga waɗanda suke fafarata, gama sun fi ni ƙarfi sosai.
Attend to my supplication, for I am brought very low; deliver me from them that persecute me; for they are stronger than I.
7 Ka’yantar da ni daga kurkuku, don in yabi sunanka. Ta haka masu adalci za su taru kewaye da ni saboda alherinka gare ni.
Bring my soul out of prison, that I may give thanks to your name, O Lord; the righteous shall wait for me, until you recompense me.

< Zabura 142 >