< Zabura 142 >

1 Maskil ne ta Dawuda. Sa’ad da yake cikin kogo. Addu’a ce. Na yi kuka mai ƙarfi ga Ubangiji; na tā da muryata ga Ubangiji neman jinƙai.
Maschil of David, when he was in the cave; a Prayer. I cry with my voice unto Jehovah; With my voice unto Jehovah do I make supplication.
2 Na kawo gunagunina a gabansa; a gabansa na faɗa wahalata.
I pour out my complaint before him; I show before him my trouble.
3 Sa’ad da ƙarfina ya kāre a cikina, kai ne wanda ya san hanyata. A hanyar da nake tafiya mutane sun kafa mini tarko.
When my spirit was overwhelmed within me, Thou knewest my path. In the way wherein I walk Have they hidden a snare for me.
4 Duba ta damata ka gani; babu wanda ya kula da ni. Ba ni da mafaka; babu wanda ya kula da raina.
Look on [my] right hand, and see; For there is no man that knoweth me: Refuge hath failed me; No man careth for my soul.
5 Na yi kuka gare ka, ya Ubangiji; Na ce, “Kai ne mafakata, rabona a ƙasar masu rai.”
I cried unto thee, O Jehovah; I said, Thou art my refuge, My portion in the land of the living.
6 Ka saurari kukata, gama ina cikin matsananciyar bukata; ka cece ni daga waɗanda suke fafarata, gama sun fi ni ƙarfi sosai.
Attend unto my cry; For I am brought very low: Deliver me from my persecutors; For they are stronger than I.
7 Ka’yantar da ni daga kurkuku, don in yabi sunanka. Ta haka masu adalci za su taru kewaye da ni saboda alherinka gare ni.
Bring my soul out of prison, That I may give thanks unto thy name: The righteous shall compass me about; For thou wilt deal bountifully with me.

< Zabura 142 >