< Zabura 141 >

1 Zabura ta Dawuda. Na yi kira gare ka, ya Ubangiji; ka zo da sauri. Ka ji muryata sa’ad da na yi kira.
مزمور داود ای خداوند تو را می‌خوانم. نزد من بشتاب! و چون تو را بخوانم آوازمرا بشنو!۱
2 Bari a sa addu’ata a gabanka kamar turaren ƙonawa; bari ɗagawa hannuwana ta zama kamar hadayar yamma.
دعای من به حضور تو مثل بخورآراسته شود، و برافراشتن دستهایم، مثل هدیه شام.۲
3 Ka sa mai tsaro a bakina, ya Ubangiji; ka yi tsaron ƙofar leɓunana.
‌ای خداوند، بر دهان من نگاهبانی فرما و درلبهایم را نگاه دار.۳
4 Kada ka bar zuciyata ta juya ga yin abin da yake mugu, ta sa kai ga aikata mugayen ayyuka tare da mutane masu aikata mugunta; kada ka bari in ci abincinsu.
دل مرا به عمل بد مایل مگردان تا مرتکب اعمال زشت با مردان بدکارنشوم. و از چیزهای لذیذ ایشان نخورم.۴
5 Bari mutum mai adalci yă buge ni, alheri ne; bar shi yă tsawata mini, mai ne a kaina. Kaina ba zai ƙi shi ba, duk da haka addu’ata kullum tana gāba da mugayen ayyuka.
مرد عادل مرا بزند و لطف خواهد بود، و مرا تادیب نماید و روغن برای سر خواهد بود! و سر من آن راابا نخواهد نمود زیرا که در بدیهای ایشان نیزدعای من دایم خواهد بود.۵
6 Za a jefar da masu mulkinsu ƙasa daga ƙwanƙolin dutse, mugaye kuwa za su san cewa maganata daidai ne.
چون داوران ایشان از سر صخره‌ها انداخته شوند، آنگاه سخنان مراخواهند شنید زیرا که شیرین است.۶
7 Za su ce, “Kamar yadda mutum kan yi huda yă tsage ƙasa, haka aka watsar da ƙasusuwanmu a bakin kabari.” (Sheol h7585)
مثل کسی‌که زمین را فلاحت و شیار بکند، استخوانهای مابر سر قبرها پراکنده می‌شود. (Sheol h7585)۷
8 Amma na kafa idanuna a kanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka; a cikinka ina neman mafaka, kada ka miƙa ni ga mutuwa.
زیرا که‌ای یهوه خداوند، چشمان من بسوی توست. و بر تو توکل دارم. پس جان مرا تلف منما!۸
9 Ka kiyaye ni daga tarkon da aka sa mini, daga tarkon da mugaye suka sa.
مرا از دامی که برای من نهاده‌اند نگاه دار و از کمندهای گناهکاران.۹
10 Bari mugaye su fāɗa a cikin ragarsu, amma bari ni in zo in wuce lafiya.
شریران به دامهای خود بیفتند و من بسلامتی در بگذرم.۱۰

< Zabura 141 >