< Zabura 141 >
1 Zabura ta Dawuda. Na yi kira gare ka, ya Ubangiji; ka zo da sauri. Ka ji muryata sa’ad da na yi kira.
A Psalm of David. O Lord, I have cried to you; hear me: attend to the voice of my supplication, when I cry to you.
2 Bari a sa addu’ata a gabanka kamar turaren ƙonawa; bari ɗagawa hannuwana ta zama kamar hadayar yamma.
Let my prayer be set forth before you as incense; the lifting up of my hands [as] an evening sacrifice.
3 Ka sa mai tsaro a bakina, ya Ubangiji; ka yi tsaron ƙofar leɓunana.
Set a watch, O Lord, on my mouth, and a strong door about by lips.
4 Kada ka bar zuciyata ta juya ga yin abin da yake mugu, ta sa kai ga aikata mugayen ayyuka tare da mutane masu aikata mugunta; kada ka bari in ci abincinsu.
Incline not my heart to evil things, to employ pretexts for sins, with me who work iniquity: and I will not. let me not unite with their choice ones.
5 Bari mutum mai adalci yă buge ni, alheri ne; bar shi yă tsawata mini, mai ne a kaina. Kaina ba zai ƙi shi ba, duk da haka addu’ata kullum tana gāba da mugayen ayyuka.
The righteous shall chasten me with mercy, and reprove me: but let not the oil of the sinner anoint my head: for yet shall my prayer also be in their pleasures.
6 Za a jefar da masu mulkinsu ƙasa daga ƙwanƙolin dutse, mugaye kuwa za su san cewa maganata daidai ne.
Their mighty ones have been swallowed up near the rock: they shall hear my words, for they are sweet.
7 Za su ce, “Kamar yadda mutum kan yi huda yă tsage ƙasa, haka aka watsar da ƙasusuwanmu a bakin kabari.” (Sheol )
As a lump of earth is crushed upon the ground, our bones have been scattered by the [mouth of] the grave. (Sheol )
8 Amma na kafa idanuna a kanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka; a cikinka ina neman mafaka, kada ka miƙa ni ga mutuwa.
For mine eyes are to you, O Lord God: I have hoped in you; take not away my life.
9 Ka kiyaye ni daga tarkon da aka sa mini, daga tarkon da mugaye suka sa.
Keep me from the snare which they have set for me, and from the stumbling blocks of them that work iniquity.
10 Bari mugaye su fāɗa a cikin ragarsu, amma bari ni in zo in wuce lafiya.
Sinners shall fall by their own net: I am alone until I shall escape.