< Zabura 141 >

1 Zabura ta Dawuda. Na yi kira gare ka, ya Ubangiji; ka zo da sauri. Ka ji muryata sa’ad da na yi kira.
I have cried to the, O Lord, hear me: hearken to my voice, when I cry to thee.
2 Bari a sa addu’ata a gabanka kamar turaren ƙonawa; bari ɗagawa hannuwana ta zama kamar hadayar yamma.
Let my prayer be directed as incense in thy sight; the lifting up of my hands, as evening sacrifice.
3 Ka sa mai tsaro a bakina, ya Ubangiji; ka yi tsaron ƙofar leɓunana.
Set a watch, O Lord, before my mouth: and a door round about my lips.
4 Kada ka bar zuciyata ta juya ga yin abin da yake mugu, ta sa kai ga aikata mugayen ayyuka tare da mutane masu aikata mugunta; kada ka bari in ci abincinsu.
Incline not my heart to evil words; to make excuses in sins. With men that work iniquity: and I will not communicate with the choicest of them.
5 Bari mutum mai adalci yă buge ni, alheri ne; bar shi yă tsawata mini, mai ne a kaina. Kaina ba zai ƙi shi ba, duk da haka addu’ata kullum tana gāba da mugayen ayyuka.
The just shall correct me in mercy, and shall reprove me: but let not the oil of the sinner fatten my head. For my prayer also shall still be against the things with which they are well pleased:
6 Za a jefar da masu mulkinsu ƙasa daga ƙwanƙolin dutse, mugaye kuwa za su san cewa maganata daidai ne.
Their judges falling upon the rock have been swallowed up. They shall hear my words, for they have prevailed:
7 Za su ce, “Kamar yadda mutum kan yi huda yă tsage ƙasa, haka aka watsar da ƙasusuwanmu a bakin kabari.” (Sheol h7585)
As when the thickness of the earth is broken up upon the ground: Our bones are scattered by the side of hell. (Sheol h7585)
8 Amma na kafa idanuna a kanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka; a cikinka ina neman mafaka, kada ka miƙa ni ga mutuwa.
But o to thee, O Lord, Lord, are my eyes: in thee have I put my trust, take not away my soul.
9 Ka kiyaye ni daga tarkon da aka sa mini, daga tarkon da mugaye suka sa.
Keep me from the snare, which they have laid for me, and from the stumblingblocks of them that work iniquity.
10 Bari mugaye su fāɗa a cikin ragarsu, amma bari ni in zo in wuce lafiya.
The wicked shall fall in his net: I am alone until I pass.

< Zabura 141 >