< Zabura 140 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka cece ni, ya Ubangiji, daga mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici,
För sångmästaren; en psalm av David. Rädda mig, HERRE, från onda människor, bevara mig från våldets män,
2 masu shirya maƙarƙashiya a zukatansu suna kuma kawo yaƙi kullum.
för dem som uttänka ont i sina hjärtan och dagligen rota sig samman till strid.
3 Suna sa harsunansu su yi kaifi kamar na maciji; dafin gamsheƙa yana a leɓunansu. (Sela)
De vässa sina tungor likasom ormar, huggormsgift är inom deras läppar. (Sela)
4 Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, daga hannuwan mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici waɗanda suke shirin kwashe ni a ƙafafu.
Bevara mig, HERRE, för de ogudaktigas händer, beskydda mig för våldets män, som uttänka planer för att bringa mig på fall.
5 Masu girman kai sun sa mini tarko; sun shimfiɗa igiyoyin ragarsu sun kuma shirya mini tarko a hanyata. (Sela)
Stolta människor lägga ut för mig snaror och garn; de breda ut nät invid vägens rand, giller sätta de för mig. (Sela)
6 Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.” Ka ji kukata ta neman jinƙai, ya Ubangiji.
Jag säger till HERREN: "Du är min Gud." Lyssna, o HERRE, till mina böners ljud.
7 Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mai fansana mai ƙarfi, wanda yake garkuwoyin kaina a ranar yaƙi.
HERRE, Herre, du min starka hjälp, du beskärmar mitt huvud, på stridens dag.
8 Kada ka biya wa mugaye bukatunsu, ya Ubangiji; kada ka bar shirinsu su yi nasara, in ba haka ba za su yi fariya. (Sela)
Tillstäd icke, HERRE; vad de ogudaktiga begära; låt deras anslag ej lyckas, de skulle eljest förhäva sig. (Sela)
9 Bari kawunan waɗanda suka kewaye ni su rufu da masifun da leɓunansu suka jawo.
Över de mäns huvuden, som omringa mig, må den olycka komma, som deras läppar bereda.
10 Bari garwashin wuta yă zubo a kansu; bari a jefar da su cikin wuta, cikin rami mai zurfi, kada su sāke tashi.
Eldsglöd må regna över dem; må de kastas i eld, i djup som de ej komma upp ur.
11 Kada masu ɓata suna su taɓa kahu a ƙasar; bari masifa ta farauci mutane masu rikici.
En förtalets man skall ej bestå i landet; en ond våldsman skall jagas, med slag på slag.
12 Na san cewa Ubangiji ya shirya wa matalauta adalci yana kuma yi wa mabukata adalci.
Jag vet att HERREN skall utföra den betrycktes sak och skaffa de fattiga rätt.
13 Tabbatacce masu adalci za su yabi sunanka masu aikata gaskiya kuma za su zauna a gabanka.
Ja, de rättfärdiga skola prisa ditt namn och de redliga bo inför ditt ansikte.

< Zabura 140 >