< Zabura 140 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka cece ni, ya Ubangiji, daga mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici,
Al maestro de coro. Salmo de David. Líbrame, Yahvé, del hombre malo; defiéndeme del hombre violento,
2 masu shirya maƙarƙashiya a zukatansu suna kuma kawo yaƙi kullum.
de esos que en su corazón maquinan cosas perversas, que provocan contiendas cada día;
3 Suna sa harsunansu su yi kaifi kamar na maciji; dafin gamsheƙa yana a leɓunansu. (Sela)
afilan su lengua como la serpiente, tienen veneno de áspid bajo sus labios.
4 Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, daga hannuwan mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici waɗanda suke shirin kwashe ni a ƙafafu.
Sálvame, Yahvé, de las manos del inicuo, guárdame del impío, de los que intentan hacerme caer.
5 Masu girman kai sun sa mini tarko; sun shimfiɗa igiyoyin ragarsu sun kuma shirya mini tarko a hanyata. (Sela)
Los soberbios me esconden lazos, y tienen mallas como red; me colocan trampas junto al camino.
6 Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.” Ka ji kukata ta neman jinƙai, ya Ubangiji.
Yo digo a Yahvé: Tú eres mi Dios; escucha, Yahvé, la voz de mi súplica.
7 Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mai fansana mai ƙarfi, wanda yake garkuwoyin kaina a ranar yaƙi.
Señor Yahvé, poderoso auxilio mío, Tú cubres mi cabeza en el día de la batalla.
8 Kada ka biya wa mugaye bukatunsu, ya Ubangiji; kada ka bar shirinsu su yi nasara, in ba haka ba za su yi fariya. (Sela)
No satisfagas, Yahvé, los deseos del inicuo, ni cumplas sus designios.
9 Bari kawunan waɗanda suka kewaye ni su rufu da masifun da leɓunansu suka jawo.
No levanten cabeza los que me asedian; caiga sobre ellos la malicia de sus lenguas.
10 Bari garwashin wuta yă zubo a kansu; bari a jefar da su cikin wuta, cikin rami mai zurfi, kada su sāke tashi.
Lluevan sobre ellos carbones encendidos, precipítalos en abismos, para no levantarse más.
11 Kada masu ɓata suna su taɓa kahu a ƙasar; bari masifa ta farauci mutane masu rikici.
El hombre de mala lengua no durará en la tierra; los infortunios caerán de golpe sobre el violento.
12 Na san cewa Ubangiji ya shirya wa matalauta adalci yana kuma yi wa mabukata adalci.
Sé que Yahvé tomará la defensa del desvalido, hará justicia a los pobres.
13 Tabbatacce masu adalci za su yabi sunanka masu aikata gaskiya kuma za su zauna a gabanka.
Ciertamente los justos celebrarán tu Nombre; los rectos habitarán en tu presencia.

< Zabura 140 >