< Zabura 140 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka cece ni, ya Ubangiji, daga mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici,
Salmo di Davide, [dato] al Capo de' Musici RISCUOTIMI, o Signore, dall'uomo malvagio; Guardami dall'uomo violento;
2 masu shirya maƙarƙashiya a zukatansu suna kuma kawo yaƙi kullum.
I quali macchinano de' mali nel cuore, [E] tuttodì muovono guerre.
3 Suna sa harsunansu su yi kaifi kamar na maciji; dafin gamsheƙa yana a leɓunansu. (Sela)
Aguzzano la lor lingua come il serpente; Veleno d'aspido [è] sotto alle lor labbra. (Sela)
4 Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, daga hannuwan mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici waɗanda suke shirin kwashe ni a ƙafafu.
Preservami, o Signore, dalle mani dell'empio; Guardami dall'uomo violento; Che hanno macchinato di far cadere i miei piedi.
5 Masu girman kai sun sa mini tarko; sun shimfiɗa igiyoyin ragarsu sun kuma shirya mini tarko a hanyata. (Sela)
I superbi mi hanno nascosto un laccio, e delle funi; Mi hanno tesa una rete sul sentiero; Mi hanno poste delle trappole. (Sela)
6 Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.” Ka ji kukata ta neman jinƙai, ya Ubangiji.
Io ho detto al Signore: Tu [sei] il mio Dio; O Signore, porgi l'orecchio al grido delle mie supplicazioni.
7 Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mai fansana mai ƙarfi, wanda yake garkuwoyin kaina a ranar yaƙi.
O Signore Iddio, [che sei] la forza della mia salute, Tu hai coperto il mio capo nel giorno dell'armi;
8 Kada ka biya wa mugaye bukatunsu, ya Ubangiji; kada ka bar shirinsu su yi nasara, in ba haka ba za su yi fariya. (Sela)
O Signore, non concedere agli empi ciò che desiderano; Non dar compimento a' lor disegni, [onde] s'innalzino. (Sela)
9 Bari kawunan waɗanda suka kewaye ni su rufu da masifun da leɓunansu suka jawo.
[Fa]'che la perversità delle labbra Di coloro che m'intorniano copra loro la testa.
10 Bari garwashin wuta yă zubo a kansu; bari a jefar da su cikin wuta, cikin rami mai zurfi, kada su sāke tashi.
Caggiano loro addosso carboni accesi; Trabocchili [Iddio] nel fuoco. In fosse profonde, [onde] non possano risorgere.
11 Kada masu ɓata suna su taɓa kahu a ƙasar; bari masifa ta farauci mutane masu rikici.
Non sia l'uomo maldicente stabilito in terra; Il male cacci l'uomo violento in precipizii.
12 Na san cewa Ubangiji ya shirya wa matalauta adalci yana kuma yi wa mabukata adalci.
Io so che il Signore farà ragione all'afflitto, [E] diritto a' poveri.
13 Tabbatacce masu adalci za su yabi sunanka masu aikata gaskiya kuma za su zauna a gabanka.
Certo, i giusti celebreranno il tuo Nome; Gli uomini diritti abiteranno appresso alla tua faccia.