< Zabura 140 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka cece ni, ya Ubangiji, daga mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici,
Az éneklőmesternek, Dávid zsoltára. Szabadíts meg engem, Uram, a gonosz embertől; a zsarnok férfitól védj meg engemet!
2 masu shirya maƙarƙashiya a zukatansu suna kuma kawo yaƙi kullum.
A kik gonoszt gondolnak szívökben, és minden nap háborút kezdenek.
3 Suna sa harsunansu su yi kaifi kamar na maciji; dafin gamsheƙa yana a leɓunansu. (Sela)
Nyelvöket élesítik, mint a kígyó; áspiskígyó mérge van ajkaik alatt. (Szela)
4 Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, daga hannuwan mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici waɗanda suke shirin kwashe ni a ƙafafu.
Ments meg, oh Uram, a gonosz kezétől; a zsarnok férfitól védj meg engemet! A kik megejteni szándékoznak lépéseimet.
5 Masu girman kai sun sa mini tarko; sun shimfiɗa igiyoyin ragarsu sun kuma shirya mini tarko a hanyata. (Sela)
Tőrt hánytak elém titkon a kevélyek és köteleket; hálót terítettek ösvényem szélére, hurkokat vetettek elém! (Szela)
6 Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.” Ka ji kukata ta neman jinƙai, ya Ubangiji.
Mondám az Úrnak: Istenem vagy te! Hallgasd meg Uram könyörgésem szavát!
7 Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mai fansana mai ƙarfi, wanda yake garkuwoyin kaina a ranar yaƙi.
Én Uram, Istenem, szabadításom ereje: fedezd be fejemet a háború napján!
8 Kada ka biya wa mugaye bukatunsu, ya Ubangiji; kada ka bar shirinsu su yi nasara, in ba haka ba za su yi fariya. (Sela)
Ne add meg Uram, a mit a gonosz kíván; rossz szándékát ne segítsd elő, mert felfuvalkodik! (Szela)
9 Bari kawunan waɗanda suka kewaye ni su rufu da masifun da leɓunansu suka jawo.
A körültem ólálkodóknak fejét borítsa be ajkaiknak átka.
10 Bari garwashin wuta yă zubo a kansu; bari a jefar da su cikin wuta, cikin rami mai zurfi, kada su sāke tashi.
Eleven szenek hulljanak reájok; tűzbe vesse őket, örvényekbe, fel ne keljenek!
11 Kada masu ɓata suna su taɓa kahu a ƙasar; bari masifa ta farauci mutane masu rikici.
A nyelves ember meg ne maradjon e földön; a zsarnok embert űzze a veszedelem, míg nyaka szakad.
12 Na san cewa Ubangiji ya shirya wa matalauta adalci yana kuma yi wa mabukata adalci.
Tudom, hogy felfogja az Úr a szegények ügyét, a nyomorultaknak jogát.
13 Tabbatacce masu adalci za su yabi sunanka masu aikata gaskiya kuma za su zauna a gabanka.
Csak az igazak magasztalják a te nevedet, s orczád előtt lakoznak az igazságosak.