< Zabura 140 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka cece ni, ya Ubangiji, daga mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici,
Pour la fin, psaume de David. Arrachez-moi, Seigneur, à l’homme méchant: à l’homme inique arrachez-moi.
2 masu shirya maƙarƙashiya a zukatansu suna kuma kawo yaƙi kullum.
Ceux qui ont pensé des iniquités dans leur cœur, durant tout le jour préparaient des combats.
3 Suna sa harsunansu su yi kaifi kamar na maciji; dafin gamsheƙa yana a leɓunansu. (Sela)
Ils ont aiguisé leur langue comme celle d’un serpent: le venin d’un aspic est sous leurs lèvres.
4 Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, daga hannuwan mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici waɗanda suke shirin kwashe ni a ƙafafu.
Gardez-moi, Seigneur, de la main d’un pécheur, et arrachez-moi à des hommes iniques. Ils ont pensé à ébranler mes pas;
5 Masu girman kai sun sa mini tarko; sun shimfiɗa igiyoyin ragarsu sun kuma shirya mini tarko a hanyata. (Sela)
Des hommes superbes ont caché un lacs devant moi: Et ils ont tendu des cordes en lacs, le long du chemin ils ont posé une pierre d’achoppement devant moi.
6 Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.” Ka ji kukata ta neman jinƙai, ya Ubangiji.
J’ai dit au Seigneur: C’est vous qui êtes mon Dieu; exaucez, Seigneur, la voix de ma supplication.
7 Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mai fansana mai ƙarfi, wanda yake garkuwoyin kaina a ranar yaƙi.
Seigneur, Seigneur, la force de mon salut, vous avez couvert ma tête de votre ombre au jour du combat;
8 Kada ka biya wa mugaye bukatunsu, ya Ubangiji; kada ka bar shirinsu su yi nasara, in ba haka ba za su yi fariya. (Sela)
Ne me livrez pas, Seigneur, à un pécheur contre mon désir: ils ont conspiré contre moi, ne me délaissez pas, de peur qu’ils ne triomphent.
9 Bari kawunan waɗanda suka kewaye ni su rufu da masifun da leɓunansu suka jawo.
La tête de leur circuit, le travail de leurs lèvres les couvrira eux-mêmes.
10 Bari garwashin wuta yă zubo a kansu; bari a jefar da su cikin wuta, cikin rami mai zurfi, kada su sāke tashi.
Des charbons tomberont sur eux, vous les précipiterez dans le feu: dans leurs misères, ils ne subsisteront pas.
11 Kada masu ɓata suna su taɓa kahu a ƙasar; bari masifa ta farauci mutane masu rikici.
Un homme à la langue méchante ne sera pas dirigé sur la terre: les maux saisiront un homme injuste à la mort.
12 Na san cewa Ubangiji ya shirya wa matalauta adalci yana kuma yi wa mabukata adalci.
Je sais que le Seigneur se chargera de la cause de l’homme sans secours, et de la vengeance des pauvres.
13 Tabbatacce masu adalci za su yabi sunanka masu aikata gaskiya kuma za su zauna a gabanka.
Cependant les justes glorifieront votre nom; et les hommes droits vivront avec vous.

< Zabura 140 >