< Zabura 140 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka cece ni, ya Ubangiji, daga mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici,
Au chef de musique. Psaume de David. Éternel! délivre-moi de l’homme mauvais, préserve-moi de l’homme violent,
2 masu shirya maƙarƙashiya a zukatansu suna kuma kawo yaƙi kullum.
Qui méditent le mal dans leur cœur: tous les jours ils s’assemblent pour la guerre;
3 Suna sa harsunansu su yi kaifi kamar na maciji; dafin gamsheƙa yana a leɓunansu. (Sela)
Ils affilent leur langue comme un serpent, il y a du venin d’aspic sous leurs lèvres. (Sélah)
4 Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, daga hannuwan mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici waɗanda suke shirin kwashe ni a ƙafafu.
Éternel! garde-moi des mains du méchant, préserve-moi de l’homme violent, qui méditent de faire trébucher mes pas.
5 Masu girman kai sun sa mini tarko; sun shimfiɗa igiyoyin ragarsu sun kuma shirya mini tarko a hanyata. (Sela)
Les orgueilleux m’ont caché un piège et des cordes, ils ont étendu un filet le long du chemin, ils m’ont dressé des lacets. (Sélah)
6 Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.” Ka ji kukata ta neman jinƙai, ya Ubangiji.
J’ai dit à l’Éternel: Tu es mon Dieu. Prête l’oreille, ô Éternel, à la voix de mes supplications!
7 Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mai fansana mai ƙarfi, wanda yake garkuwoyin kaina a ranar yaƙi.
L’Éternel, le Seigneur, est la force de mon salut; tu as couvert ma tête au jour des armes.
8 Kada ka biya wa mugaye bukatunsu, ya Ubangiji; kada ka bar shirinsu su yi nasara, in ba haka ba za su yi fariya. (Sela)
N’accorde pas, ô Éternel! les souhaits du méchant, ne fais pas réussir son dessein: ils s’élèveraient. (Sélah)
9 Bari kawunan waɗanda suka kewaye ni su rufu da masifun da leɓunansu suka jawo.
Quant à la tête de ceux qui m’environnent, … que le mal de leurs lèvres les couvre,
10 Bari garwashin wuta yă zubo a kansu; bari a jefar da su cikin wuta, cikin rami mai zurfi, kada su sāke tashi.
Que des charbons ardents tombent sur eux! Fais-les tomber dans le feu, dans des eaux profondes, et qu’ils ne se relèvent pas!
11 Kada masu ɓata suna su taɓa kahu a ƙasar; bari masifa ta farauci mutane masu rikici.
Que l’homme à [mauvaise] langue ne soit point établi dans le pays: l’homme violent, le mal le poussera à sa ruine.
12 Na san cewa Ubangiji ya shirya wa matalauta adalci yana kuma yi wa mabukata adalci.
Je sais que l’Éternel maintiendra la cause de l’affligé, le jugement des pauvres.
13 Tabbatacce masu adalci za su yabi sunanka masu aikata gaskiya kuma za su zauna a gabanka.
Certainement, les justes célébreront ton nom, les hommes droits habiteront devant toi.