< Zabura 140 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka cece ni, ya Ubangiji, daga mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici,
To the leader. A Psalm of David. Rescue me, Lord, from evil people; from the violent guard me
2 masu shirya maƙarƙashiya a zukatansu suna kuma kawo yaƙi kullum.
from those who plot evil in their heart, and stir up war continually:
3 Suna sa harsunansu su yi kaifi kamar na maciji; dafin gamsheƙa yana a leɓunansu. (Sela)
who make their tongue as sharp as a serpent’s, and under whose lips is the poison of adders. (Selah)
4 Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, daga hannuwan mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici waɗanda suke shirin kwashe ni a ƙafafu.
Preserve me, O Lord, from the hands of the wicked, from the violent guard me from those who are plotting to trip up my feet.
5 Masu girman kai sun sa mini tarko; sun shimfiɗa igiyoyin ragarsu sun kuma shirya mini tarko a hanyata. (Sela)
The proud have hidden a trap for me, cords they have spread as a net for my feet: snares they have set at the side of my track. (Selah)
6 Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.” Ka ji kukata ta neman jinƙai, ya Ubangiji.
I have said to the Lord, “My God are you; attend, Lord, to my loud plea.
7 Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mai fansana mai ƙarfi, wanda yake garkuwoyin kaina a ranar yaƙi.
O Lord my Lord, my savior mighty, you did cover my head in the day of battle.
8 Kada ka biya wa mugaye bukatunsu, ya Ubangiji; kada ka bar shirinsu su yi nasara, in ba haka ba za su yi fariya. (Sela)
Grant not, O Lord, the desires of the wicked; and what they have purposed, promote you not.” (Selah)
9 Bari kawunan waɗanda suka kewaye ni su rufu da masifun da leɓunansu suka jawo.
Let them not lift up their heads against me. May the mischief they prate bring themselves to destruction,
10 Bari garwashin wuta yă zubo a kansu; bari a jefar da su cikin wuta, cikin rami mai zurfi, kada su sāke tashi.
may he rain upon them coals of fire, may he strike them down swiftly, to rise no more,
11 Kada masu ɓata suna su taɓa kahu a ƙasar; bari masifa ta farauci mutane masu rikici.
no place in the land may there be for the slanderer: may the violent be hunted from sorrow to sorrow.
12 Na san cewa Ubangiji ya shirya wa matalauta adalci yana kuma yi wa mabukata adalci.
I know that the Lord will do right by the weak, and will execute justice for those who are needy.
13 Tabbatacce masu adalci za su yabi sunanka masu aikata gaskiya kuma za su zauna a gabanka.
Surely the righteous shall praise your name, and they who are upright shall live in your presence.