< Zabura 140 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka cece ni, ya Ubangiji, daga mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici,
For the Chief Musician. A Psalm of David. Deliver me, O Jehovah, from the evil man; Preserve me from the violent man:
2 masu shirya maƙarƙashiya a zukatansu suna kuma kawo yaƙi kullum.
Who devise mischiefs in their heart; Continually do they gather themselves together for war.
3 Suna sa harsunansu su yi kaifi kamar na maciji; dafin gamsheƙa yana a leɓunansu. (Sela)
They have sharpened their tongue like a serpent; Adders’ poison is under their lips. (Selah)
4 Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, daga hannuwan mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici waɗanda suke shirin kwashe ni a ƙafafu.
Keep me, O Jehovah, from the hands of the wicked; Preserve me from the violent man: Who have purposed to thrust aside my steps.
5 Masu girman kai sun sa mini tarko; sun shimfiɗa igiyoyin ragarsu sun kuma shirya mini tarko a hanyata. (Sela)
The proud have hid a snare for me, and cords; They have spread a net by the wayside; They have set gins for me. (Selah)
6 Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.” Ka ji kukata ta neman jinƙai, ya Ubangiji.
I said unto Jehovah, Thou art my God: Give ear unto the voice of my supplications, O Jehovah.
7 Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mai fansana mai ƙarfi, wanda yake garkuwoyin kaina a ranar yaƙi.
O Jehovah the Lord, the strength of my salvation, Thou hast covered my head in the day of battle.
8 Kada ka biya wa mugaye bukatunsu, ya Ubangiji; kada ka bar shirinsu su yi nasara, in ba haka ba za su yi fariya. (Sela)
Grant not, O Jehovah, the desires of the wicked; Further not his evil device, [lest] they exalt themselves. (Selah)
9 Bari kawunan waɗanda suka kewaye ni su rufu da masifun da leɓunansu suka jawo.
As for the head of those that compass me about, Let the mischief of their own lips cover them.
10 Bari garwashin wuta yă zubo a kansu; bari a jefar da su cikin wuta, cikin rami mai zurfi, kada su sāke tashi.
Let burning coals fall upon them: Let them be cast into the fire, Into deep pits, whence they shall not rise.
11 Kada masu ɓata suna su taɓa kahu a ƙasar; bari masifa ta farauci mutane masu rikici.
An evil speaker shall not be established in the earth: Evil shall hunt the violent man to overthrow him.
12 Na san cewa Ubangiji ya shirya wa matalauta adalci yana kuma yi wa mabukata adalci.
I know that Jehovah will maintain the cause of the afflicted, And justice for the needy.
13 Tabbatacce masu adalci za su yabi sunanka masu aikata gaskiya kuma za su zauna a gabanka.
Surely the righteous shall give thanks unto thy name: The upright shall dwell in thy presence.

< Zabura 140 >