< Zabura 14 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Wawaye sukan ce a ransu, “Ba Allah.” Sun lalace, ayyukansu kuwa mugaye ne; babu wani da yake yi abu mai kyau.
برای رهبر سرایندگان. مزمور داوود. کسی که فکر می‌کند خدایی نیست، ابله است. چنین شخصی فاسد است و دست به کارهای پلید می‌زند و هیچ نیکی در او نیست.
2 Ubangiji ya duba daga sama a kan’yan adam don yă ga ko akwai wani da ya gane, wani wanda yake neman Allah.
خداوند از آسمان به انسانها نگاه می‌کند تا شخص فهمیده‌ای بیابد که طالب خدا باشد.
3 Duka sun kauce, duka gaba ɗaya sun zama lalatattu; babu ɗaya wanda yake yin abu mai kyau, ba ko ɗaya.
اما همه گمراه شده‌اند، همه فاسد گشته‌اند، نیکوکاری نیست، حتی یک نفر.
4 Masu aikata mugunta za su taɓa koyo. Suna cin mutane yadda mutane ke cin gurasa kuma waɗanda ba sa kira bisa Ubangiji?
آیا این بدکاران شعور ندارند؟ آنها که قوم مرا مانند نان می‌بلعند و می‌خورند و هرگز خداوند را نمی‌طلبند؟
5 Ga su, tsoro ya sha kansu, gama Allah yana cikin ƙungiyar adalai.
ولی وحشت، آنها را فرا می‌گیرد زیرا خدا با درستکاران است.
6 Ku masu mugunta kuna sa ƙoƙarin matalauta yă zama banza, amma Ubangiji ne mafakansu.
بله، وقتی بدکاران امید آدم بیچاره را نقش بر آب می‌کنند، خداوند او را در پناه خود می‌گیرد.
7 Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Ubangiji zai maido da sa’ar mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!
کاش که نجات برای اسرائیل از صهیون فرا می‌رسید و خداوند سعادت گذشته را به قوم خود باز می‌گردانید! بگذار یعقوب شادی کند و اسرائیل به وجد آید!

< Zabura 14 >