< Zabura 14 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Wawaye sukan ce a ransu, “Ba Allah.” Sun lalace, ayyukansu kuwa mugaye ne; babu wani da yake yi abu mai kyau.
Au chef des chantres; de David. L’Insensé a dit en son cœur: "Il n’est point de Dieu!" On est corrompu, on commet des actes odieux, personne ne fait le bien.
2 Ubangiji ya duba daga sama a kan’yan adam don yă ga ko akwai wani da ya gane, wani wanda yake neman Allah.
L’Eternel, du haut du ciel, regarde les hommes, pour voir s’il en est de bien inspirés, recherchant Dieu.
3 Duka sun kauce, duka gaba ɗaya sun zama lalatattu; babu ɗaya wanda yake yin abu mai kyau, ba ko ɗaya.
Tous ils ont dévié, ensemble ils sont pervertis; personne n’agit bien, pas même un seul.
4 Masu aikata mugunta za su taɓa koyo. Suna cin mutane yadda mutane ke cin gurasa kuma waɗanda ba sa kira bisa Ubangiji?
Eh bien! Ils s’en ressentiront, tous ces ouvriers d’iniquité, qui dévorent mon peuple comme on mange du pain, et n’invoquent point l’Eternel.
5 Ga su, tsoro ya sha kansu, gama Allah yana cikin ƙungiyar adalai.
Dès lors, ils seront saisis d’épouvante, car Dieu est avec la race des justes.
6 Ku masu mugunta kuna sa ƙoƙarin matalauta yă zama banza, amma Ubangiji ne mafakansu.
Pensez-vous confondre les desseins du pauvre, alors que l’Eternel est son abri?
7 Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Ubangiji zai maido da sa’ar mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!
Ah! puisse venir de Sion le salut d’Israël! Quand le Seigneur ramènera les captifs de son peuple, Jacob jubilera, Israël sera dans la joie.

< Zabura 14 >